• English
  • Business News
Thursday, August 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zulum Ya Bai Wa Matasan Biu 1,000 Tallafin Miliyan 100 Don Yin Jari

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Zulum Ya Bai Wa Matasan Biu 1,000 Tallafin Miliyan 100 Don Yin Jari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Babagana Zulum na Jihar Borno, ya ce ya bai wa matasa marasa aikin yi 1,000 tallafin Naira miliyan 100 a garin Biu.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da babban mataimaki na musamman ga gwamnan kan harkokin yada labarai, Baba-Sheik Haruna, ya sanyawa hannu kuma ya fitar a Abuja ranar Juma’a.

  • Kotu Ta Soke Takarar Dare A Matsayin Wanda Zai Yi Wa PDP Takarar Gwamna A Zamfara
  • Tagomashin Da CBN Ya Samar Wajen Bunkasa Kanana Da Matsakaitan Sana’o’i

Ya ce tallafin, wanda aka gudanar a Kadafur da ke garin Biu, za a yi amfani da shi ne a matsayin jarin fara kasuwanci ga masu kananan sana’o’i domin bunkasa tattalin arzikin yankin.

Taron dai wani bangare ne na rangadin kwanaki uku da gwamnan ya kai hedikwatar Sanatan Borno ta Kudu, domin kaddamar da ayyuka daban-daban da gwamnatinsa ta aiwatar.

A yayin da yake kira ga wadanda suka ci gajiyar tallafin da su yi amfani da wannan tallafin da idon basira, gwamnan ya ce gwamnati za ta ci gaba da kokarin rage zaman kashe wando da yaki da fatara ta hanyar taimaka wa marasa galihu da dai sauransu.

Labarai Masu Nasaba

ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A ZaÉ“en 2027 – Amaechi

Tinubu Ya Dawo Nijeriya Bayan Ziyarar Aiki A Brazil

Ya bayyana cewa talauci, rashin aikin yi da rashin ilimi ne suka taka muhimmiyar rawa wajen bullar Boko Haram a jihar.

A tsawon wannan lokaci, Zulum ya kaddamar da Makarantar Sakandaren Gwamnati ta Mega da ke Buratai mai daukar dalibai 1,500, sannan ya bude babbar makarantar Islamiyya ga dalibai 1,200 da ke Biu da kuma Sashen Sa ido da tantance Ilimi na Shiyya a garin Biu.

Tun da farko kwamishinan matasa, ci gaban wasanni da yaki da fatara, Saina Buba, ya ce an zabo wadanda suka amfana su 1,000 ne daga gundumomi a fadin karamar hukumar Biu.

Ya ce gwamnan, wanda tun a shekarar 2019, ya kaddamar da wasu tsare-tsare na tattalin arziki da ke bayar da tallafin kudi ga kanana da matsakaitan ‘yan kasuwa, bai bar masu nakasa da kuma tsofaffi ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BiuBoko HaramBornoGwamnaMatasaTalauciTallafiYaki Da FataraZulum
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Soke Takarar Dare A Matsayin Wanda Zai Yi Wa PDP Takarar Gwamna A Zamfara

Next Post

Farfadowar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Zarce Yadda Ake Tsammani

Related

ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A ZaÉ“en 2027 – Amaechi
Manyan Labarai

ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A ZaÉ“en 2027 – Amaechi

2 hours ago
Tinubu Ya Dawo Nijeriya Bayan Ziyarar Aiki A Brazil
Manyan Labarai

Tinubu Ya Dawo Nijeriya Bayan Ziyarar Aiki A Brazil

3 hours ago
Yadda Aka Cafke Masu Saka Ƙwayoyi A Jakunkunan Matafiya A Filin Jirgin Sama A Kano
Manyan Labarai

Yadda Aka Cafke Masu Saka Ƙwayoyi A Jakunkunan Matafiya A Filin Jirgin Sama A Kano

13 hours ago
Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 
Manyan Labarai

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

20 hours ago
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba
Manyan Labarai

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

1 day ago
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro
Manyan Labarai

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

1 day ago
Next Post
Farfadowar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Zarce Yadda Ake Tsammani

Farfadowar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Zarce Yadda Ake Tsammani

LABARAI MASU NASABA

ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A ZaÉ“en 2027 – Amaechi

ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A ZaÉ“en 2027 – Amaechi

August 28, 2025
Tinubu Ya Dawo Nijeriya Bayan Ziyarar Aiki A Brazil

Tinubu Ya Dawo Nijeriya Bayan Ziyarar Aiki A Brazil

August 28, 2025
Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

August 27, 2025
Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci

Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci

August 27, 2025
Yadda Aka Cafke Masu Saka Ƙwayoyi A Jakunkunan Matafiya A Filin Jirgin Sama A Kano

Yadda Aka Cafke Masu Saka Ƙwayoyi A Jakunkunan Matafiya A Filin Jirgin Sama A Kano

August 27, 2025
Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi

Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi

August 27, 2025
Jimilar Darajar Hada-Hadar Shige Da Fice A Fannin Bayar Da Hidimomi Ta Kasar Sin Ta Kai Yuan Tiriliyan 3.9 A Rabin Farko Na Shekarar Bana

Jimilar Darajar Hada-Hadar Shige Da Fice A Fannin Bayar Da Hidimomi Ta Kasar Sin Ta Kai Yuan Tiriliyan 3.9 A Rabin Farko Na Shekarar Bana

August 27, 2025
Gwamnan Katsina Ya Dawo Gida Domin Ziyara Ga Al’ummar Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Malumfashi

Gwamnan Katsina Ya Dawo Gida Domin Ziyara Ga Al’ummar Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Malumfashi

August 27, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

August 27, 2025
Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

August 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.