• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Ta Barazanar Kashe Ni Kan Shaidar Katin Dan Kasa Da Rijistar Layuka – Pantami

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
An Yi Ta Barazanar Kashe Ni Kan Shaidar Katin Dan Kasa Da Rijistar Layuka – Pantami
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan sadarwa, Farfesa Isa Ali Pantami, ya bayyana cewar, an yi ta tura masa sakonnin barazanar kisa kawai don aiwatar katin shaidar dan kasa (NIN) da rijistar tantance masu amfani da layukan waya a fadin kasar nan. 

Pantami wadda ya shaida hakan a wajen taron shekara-shekarashekara-shekara na karo na hudu wanda ake yi duk ranar 16 g watan Satumban kuma hukumar kula da shaidar katin dan kasa (NIMC) ta gudanar a Abuja.

  • CAN Ta Yi Allah Wadai Da Harin Da Aka Kai Wa Hadimin Gwamnan Bauchi

Ya ce sun maida hankali wajen amfani da fasahar sadarwar zamani wajen taskace bayanai tare da karfafa ‘yan kasa da su rungumi hakan amma wasu mutane kuma sai suka juya kansa wadda hakan bai musu yadda suke so ba.

“An yi ta barazana ga rayuwata saboda gabatar da tsarin NIN da rijistan layuka. Na yi imanin babu wani da zai iya sarrafa rayuwata a duk duniyar nan, Allah ne kadai. Mun dake kuma yanzu haka tsarin na aiki.

“Wasu lokutan na kan iya kwashe wata guda ma ba tare da na yi magana da NIMC ba kuma babu wata matsala. A yau, mafiya yawan wadanda muka yaka yanzu sun yi tsit. Idan aka koma shekaru uku aka yi waiwaye, hukumar kula da shaidar dan kasa (NIMC) na aiki ne cikin mawuyacin hali, don cimma alkaluman rijista ga kusan miliyan 90 ga kasar.

Labarai Masu Nasaba

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

“A lokacin da na fara kula da NIMC adadin cibiyoyin rijista ba su wuce 1,000 ba, amma a yanzu, muna sa sama da 50,000. Tsarin taskace bayanai na tafiya yadda ya kamata. Mun kafa manufofin da tsare-tsaren kasa guda 19 kuma dukkaninsu an aiwatar. A tarihin Nijeriya ba a taba samun hakan ba,” Inji Ministan.

Ya bayyana cewar sashin ICT ya bada gudunmawa kaso 18.44% na kudaden shigar Nijeriya a 2022.

Darakta-janar na hukumar NIMC, Injiniya Aliyu Abdulaziz, ya ce suna hadin guiwa da sarakuna domin kara wayar da kan al’umman musamman na yankunan karkara da kan muhimmanci rijistan NIN.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BarazanaKatin Dan KasaLayiPantami
ShareTweetSendShare
Previous Post

CAN Ta Yi Allah Wadai Da Harin Da Aka Kai Wa Hadimin Gwamnan Bauchi

Next Post

‘Yan Bindigan Da Ake Fatattaka Daga Arewa Maso Yamma Na Kwararowa Arewa Maso Gabas – Gwamnoni

Related

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

8 hours ago
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

12 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

13 hours ago
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kai Ziyarar Aiki Jihar Anambra

15 hours ago
APC: Na Bar PDP Ne Domin Ci Gaba Da Amfana Da Ribar Ofishi Na – Kakakin Majalisar Edo
Manyan Labarai

APC: Na Bar PDP Ne Domin Ci Gaba Da Amfana Da Ribar Ofishi Na – Kakakin Majalisar Edo

2 days ago
Kwanaki 40: Iyalan Maharban Da Aka Kashe A Edo Na Neman A Biya Su Diyya
Manyan Labarai

Kwanaki 40: Iyalan Maharban Da Aka Kashe A Edo Na Neman A Biya Su Diyya

2 days ago
Next Post
Gwamnonin Arewa Maso Gabas Za Su Samar Da Kamfanin Zirga-zirgan Jirgin Sama

'Yan Bindigan Da Ake Fatattaka Daga Arewa Maso Yamma Na Kwararowa Arewa Maso Gabas - Gwamnoni

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

May 8, 2025
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

May 8, 2025
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

May 8, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

May 8, 2025
An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.