• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Biyayya Ga Umarnin Allah Ne Kadai Zai Kawo Karshen Matsalolin Nijeriya —Sheikh Yusuf Ali

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Allah

Sheikh Dr Yusuf Ali, ya bayyana cewar yin aiki da Dokokin Allah su ne kawai mafitar da za su kawo karshen matsalolin da suke addabar kasar nan ta Nijeriya.

Ali wadda shine Sarkin Malaman masarautar Gaya ya bayyana hakan ne a lokacin da yake hira ta musamman da ‘yan jarida akan karramawar da Gidauniyar ‘Ganduje Foundation’ ta yi masa kan hidimar da ya ke yi wajen isar da sakon Allah (SAW) a ranar Juma’a a zawiyyarsa dake Unguwar Tudun Maliki a cikin birnin Kano inda ya samu halartar’ ‘yan jaridu da kuma wasu muridan Shehin Malamin.

  • Daukakar Nasaba Da Girman Garin Annabi Muhammadu (SAW)

An karrama Shehin Malamin ne a yayin rufe musabakar Alkur’ani da Gidauniyar Ganduje take shiryawa a kowacce shekara.

Shehin Malamin ya jaddada cewa: “Babu wata madogara yanzu a dukkanin al’ummar duniya baki daya, Musulmi da wadanda ba Musulmi ba illa wannan addinin, da kuma wannan littafin (Kur’ani). Duk wadansu tsare-tsare da wadansu bincike-bincike da duk wani abu da za a gwada, an gwada, amma duniyar nan ga halin da ake ciki, haka take, sama da kasa, a birkice, ba a samu yadda ake so ba.

“Saboda haka babu wani wata fata ga al’ummar yanzu da wadanda za su zo nan gaba illa wannan addini da kuma wannan littafi,” ya tabbatar.

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

Ya kara da cewa, “Duk wani bincike da aka yi a duniyar nan, komai zurfinsa, duk mamakinsa, duk sararin samaniyyar da aka tafi, duk kasar da aka tafi, duk abin da aka kirkiro, za ka samu Alkur’ani ya yi bayaninsa dalla-dalla. A bakin wa aka ji? A bakin Manzo Allah (SAW),” ya nusasshe.

Ya lurantar da cewa ka da kawai a tsaya a karanta Alkur’ani, a ci gaba da zurfafa bincike, Alkur’anin zai warware dukkannin matsalolinmu baki daya.

“Mu yi koyi da shi kamar yadda dabi’un Manzon Allah (SAW) da halayyarsa ya kasance Alkur’anin ne. Duk abin da Alkur’ani ya hana, ya hanu, duk abin da Alkur’ani ya ce ya yi shi ne yake yi. Ba abin da Alkur’ani ya bari.

“Duk abin da za mu yi ya kasance Kur’ani shi ne zai kasance ya zama jagoranmu. Abin da ya ce mu yi shi ne za mu yi. Za a ga abubuwa sun rincabe baki daya. Saboda mene? Saboda wanda ya halicce mu ya ce ga abin da za a yi a cikin littafinsa na karshe, bamu yi.

“Annabin da ya aiko na karshe babu wani Annabin bayanshi. Mune al’ummar karshe. Amma kuma ba ma bin abin da ya ce. Mu koma wannan littafi ga baki daya, ya zama shi ne zai zame mana mizani a shugabancinmu, a mulkinmu, a sana’armu, a nomannu, a aurenmu, a tarbiyyarmu, a huldarmu da jama’a. Abin da ya shafi lafiyarmu, da abin da ya shafi duk wani hali na siyarmu da sauran su.”

Sheikh Yusuf Ali ya kara da cewa, makasudin ba shi wannan lambar girmama shi ne; saboda hidimar da yake gudanarwa shekara da shekaru wajen daukaka addinin Musulunci tare da zaburarwa da karfafawa kan karatun Alkur’ani mai girma.

Shehin Malamin ya ce yana godiya ga Allah ta’ala bisa shiriyar da shi da ya yi da littafin Alkur’ani mai girma.

Shaikh Dr Yusuf Ali har, ya cigaba da cewa, ba yau ne farkon ba shi kyauta da Gwamna Ganduje ya yi masa ba. Amma ya ce wannan ta sha bamban saboda an ba shi ne kan Alkur’ani.

Ya mika godiyarsa ga Gwamna Abdullahi Umar Ganduje bisa wannan karammawar.

Sai ya yi kira ga sauran gwamnoni da shugabanni a matakai daban-daban da su bunkasa addinin Musulunci da karfafawa masu kokarin haddace Alkur’ani guiwa.

Gidauniyar ta Ganduje ta kasance tana ilmantarwa da karfafawa mutane karatun Alkur’ani, da gina makarantu da masallatai tare da musuluntar da wadanda ba Musulmi ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya
Rahotonni

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

October 4, 2025
Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin
Rahotonni

Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin

October 3, 2025
Next Post
Yadda Amurka Da Birtaniya Da Australiya Ke Baza Nukiliya Abu Ne Mai Hadari

Yadda Amurka Da Birtaniya Da Australiya Ke Baza Nukiliya Abu Ne Mai Hadari

LABARAI MASU NASABA

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.