ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Biyayya Ga Umarnin Allah Ne Kadai Zai Kawo Karshen Matsalolin Nijeriya —Sheikh Yusuf Ali

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Allah

Sheikh Dr Yusuf Ali, ya bayyana cewar yin aiki da Dokokin Allah su ne kawai mafitar da za su kawo karshen matsalolin da suke addabar kasar nan ta Nijeriya.

Ali wadda shine Sarkin Malaman masarautar Gaya ya bayyana hakan ne a lokacin da yake hira ta musamman da ‘yan jarida akan karramawar da Gidauniyar ‘Ganduje Foundation’ ta yi masa kan hidimar da ya ke yi wajen isar da sakon Allah (SAW) a ranar Juma’a a zawiyyarsa dake Unguwar Tudun Maliki a cikin birnin Kano inda ya samu halartar’ ‘yan jaridu da kuma wasu muridan Shehin Malamin.

  • Daukakar Nasaba Da Girman Garin Annabi Muhammadu (SAW)

An karrama Shehin Malamin ne a yayin rufe musabakar Alkur’ani da Gidauniyar Ganduje take shiryawa a kowacce shekara.

ADVERTISEMENT

Shehin Malamin ya jaddada cewa: “Babu wata madogara yanzu a dukkanin al’ummar duniya baki daya, Musulmi da wadanda ba Musulmi ba illa wannan addinin, da kuma wannan littafin (Kur’ani). Duk wadansu tsare-tsare da wadansu bincike-bincike da duk wani abu da za a gwada, an gwada, amma duniyar nan ga halin da ake ciki, haka take, sama da kasa, a birkice, ba a samu yadda ake so ba.

“Saboda haka babu wani wata fata ga al’ummar yanzu da wadanda za su zo nan gaba illa wannan addini da kuma wannan littafi,” ya tabbatar.

LABARAI MASU NASABA

Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ya kara da cewa, “Duk wani bincike da aka yi a duniyar nan, komai zurfinsa, duk mamakinsa, duk sararin samaniyyar da aka tafi, duk kasar da aka tafi, duk abin da aka kirkiro, za ka samu Alkur’ani ya yi bayaninsa dalla-dalla. A bakin wa aka ji? A bakin Manzo Allah (SAW),” ya nusasshe.

Ya lurantar da cewa ka da kawai a tsaya a karanta Alkur’ani, a ci gaba da zurfafa bincike, Alkur’anin zai warware dukkannin matsalolinmu baki daya.

“Mu yi koyi da shi kamar yadda dabi’un Manzon Allah (SAW) da halayyarsa ya kasance Alkur’anin ne. Duk abin da Alkur’ani ya hana, ya hanu, duk abin da Alkur’ani ya ce ya yi shi ne yake yi. Ba abin da Alkur’ani ya bari.

“Duk abin da za mu yi ya kasance Kur’ani shi ne zai kasance ya zama jagoranmu. Abin da ya ce mu yi shi ne za mu yi. Za a ga abubuwa sun rincabe baki daya. Saboda mene? Saboda wanda ya halicce mu ya ce ga abin da za a yi a cikin littafinsa na karshe, bamu yi.

“Annabin da ya aiko na karshe babu wani Annabin bayanshi. Mune al’ummar karshe. Amma kuma ba ma bin abin da ya ce. Mu koma wannan littafi ga baki daya, ya zama shi ne zai zame mana mizani a shugabancinmu, a mulkinmu, a sana’armu, a nomannu, a aurenmu, a tarbiyyarmu, a huldarmu da jama’a. Abin da ya shafi lafiyarmu, da abin da ya shafi duk wani hali na siyarmu da sauran su.”

Sheikh Yusuf Ali ya kara da cewa, makasudin ba shi wannan lambar girmama shi ne; saboda hidimar da yake gudanarwa shekara da shekaru wajen daukaka addinin Musulunci tare da zaburarwa da karfafawa kan karatun Alkur’ani mai girma.

Shehin Malamin ya ce yana godiya ga Allah ta’ala bisa shiriyar da shi da ya yi da littafin Alkur’ani mai girma.

Shaikh Dr Yusuf Ali har, ya cigaba da cewa, ba yau ne farkon ba shi kyauta da Gwamna Ganduje ya yi masa ba. Amma ya ce wannan ta sha bamban saboda an ba shi ne kan Alkur’ani.

Ya mika godiyarsa ga Gwamna Abdullahi Umar Ganduje bisa wannan karammawar.

Sai ya yi kira ga sauran gwamnoni da shugabanni a matakai daban-daban da su bunkasa addinin Musulunci da karfafawa masu kokarin haddace Alkur’ani guiwa.

Gidauniyar ta Ganduje ta kasance tana ilmantarwa da karfafawa mutane karatun Alkur’ani, da gina makarantu da masallatai tare da musuluntar da wadanda ba Musulmi ba.

Allah
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Noma
Rahotonni

Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba

June 26, 2026
Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
Next Post
Yadda Amurka Da Birtaniya Da Australiya Ke Baza Nukiliya Abu Ne Mai Hadari

Yadda Amurka Da Birtaniya Da Australiya Ke Baza Nukiliya Abu Ne Mai Hadari

LABARAI MASU NASABA

Sowore Ya Sha Alwashin Ci Gaba Da Gwagwarmaya Duk Da Tsare Shi A Gidan Yarin Kuje

Jagoran Matasan AAC Kwamret Yahaya Soje Ya Nemi A Saki Sowore

June 26, 2026
Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC

Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC

June 26, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

June 26, 2026
Noma

Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba

June 26, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

June 26, 2026
Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

June 26, 2026
Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

June 26, 2026
Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.