ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Biyayya Ga Umarnin Allah Ne Kadai Zai Kawo Karshen Matsalolin Nijeriya —Sheikh Yusuf Ali

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Allah

Sheikh Dr Yusuf Ali, ya bayyana cewar yin aiki da Dokokin Allah su ne kawai mafitar da za su kawo karshen matsalolin da suke addabar kasar nan ta Nijeriya.

Ali wadda shine Sarkin Malaman masarautar Gaya ya bayyana hakan ne a lokacin da yake hira ta musamman da ‘yan jarida akan karramawar da Gidauniyar ‘Ganduje Foundation’ ta yi masa kan hidimar da ya ke yi wajen isar da sakon Allah (SAW) a ranar Juma’a a zawiyyarsa dake Unguwar Tudun Maliki a cikin birnin Kano inda ya samu halartar’ ‘yan jaridu da kuma wasu muridan Shehin Malamin.

  • Daukakar Nasaba Da Girman Garin Annabi Muhammadu (SAW)

An karrama Shehin Malamin ne a yayin rufe musabakar Alkur’ani da Gidauniyar Ganduje take shiryawa a kowacce shekara.

ADVERTISEMENT

Shehin Malamin ya jaddada cewa: “Babu wata madogara yanzu a dukkanin al’ummar duniya baki daya, Musulmi da wadanda ba Musulmi ba illa wannan addinin, da kuma wannan littafin (Kur’ani). Duk wadansu tsare-tsare da wadansu bincike-bincike da duk wani abu da za a gwada, an gwada, amma duniyar nan ga halin da ake ciki, haka take, sama da kasa, a birkice, ba a samu yadda ake so ba.

“Saboda haka babu wani wata fata ga al’ummar yanzu da wadanda za su zo nan gaba illa wannan addini da kuma wannan littafi,” ya tabbatar.

LABARAI MASU NASABA

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

Ya kara da cewa, “Duk wani bincike da aka yi a duniyar nan, komai zurfinsa, duk mamakinsa, duk sararin samaniyyar da aka tafi, duk kasar da aka tafi, duk abin da aka kirkiro, za ka samu Alkur’ani ya yi bayaninsa dalla-dalla. A bakin wa aka ji? A bakin Manzo Allah (SAW),” ya nusasshe.

Ya lurantar da cewa ka da kawai a tsaya a karanta Alkur’ani, a ci gaba da zurfafa bincike, Alkur’anin zai warware dukkannin matsalolinmu baki daya.

“Mu yi koyi da shi kamar yadda dabi’un Manzon Allah (SAW) da halayyarsa ya kasance Alkur’anin ne. Duk abin da Alkur’ani ya hana, ya hanu, duk abin da Alkur’ani ya ce ya yi shi ne yake yi. Ba abin da Alkur’ani ya bari.

“Duk abin da za mu yi ya kasance Kur’ani shi ne zai kasance ya zama jagoranmu. Abin da ya ce mu yi shi ne za mu yi. Za a ga abubuwa sun rincabe baki daya. Saboda mene? Saboda wanda ya halicce mu ya ce ga abin da za a yi a cikin littafinsa na karshe, bamu yi.

“Annabin da ya aiko na karshe babu wani Annabin bayanshi. Mune al’ummar karshe. Amma kuma ba ma bin abin da ya ce. Mu koma wannan littafi ga baki daya, ya zama shi ne zai zame mana mizani a shugabancinmu, a mulkinmu, a sana’armu, a nomannu, a aurenmu, a tarbiyyarmu, a huldarmu da jama’a. Abin da ya shafi lafiyarmu, da abin da ya shafi duk wani hali na siyarmu da sauran su.”

Sheikh Yusuf Ali ya kara da cewa, makasudin ba shi wannan lambar girmama shi ne; saboda hidimar da yake gudanarwa shekara da shekaru wajen daukaka addinin Musulunci tare da zaburarwa da karfafawa kan karatun Alkur’ani mai girma.

Shehin Malamin ya ce yana godiya ga Allah ta’ala bisa shiriyar da shi da ya yi da littafin Alkur’ani mai girma.

Shaikh Dr Yusuf Ali har, ya cigaba da cewa, ba yau ne farkon ba shi kyauta da Gwamna Ganduje ya yi masa ba. Amma ya ce wannan ta sha bamban saboda an ba shi ne kan Alkur’ani.

Ya mika godiyarsa ga Gwamna Abdullahi Umar Ganduje bisa wannan karammawar.

Sai ya yi kira ga sauran gwamnoni da shugabanni a matakai daban-daban da su bunkasa addinin Musulunci da karfafawa masu kokarin haddace Alkur’ani guiwa.

Gidauniyar ta Ganduje ta kasance tana ilmantarwa da karfafawa mutane karatun Alkur’ani, da gina makarantu da masallatai tare da musuluntar da wadanda ba Musulmi ba.

Allah
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Umarnin Kawo Karshen Matsalar Tsaro
Rahotonni

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

September 5, 2026
Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
Rahotonni

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

September 5, 2026
Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
Rahotonni

Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki

September 5, 2026
Next Post
Yadda Amurka Da Birtaniya Da Australiya Ke Baza Nukiliya Abu Ne Mai Hadari

Yadda Amurka Da Birtaniya Da Australiya Ke Baza Nukiliya Abu Ne Mai Hadari

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.