ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin

Arewa Maso Yamma Na Da Dalibai 157,831, Arewa Maso Gabas

by Sani Anwar
9 months ago
Bashin

Arewa Maso Yamma Na Da Dalibai 157,831, Arewa Maso Gabas 127,058, Kudu Maso Yamma 92,850, Arewa Ta Tsakiya 74,120, Kudu Maso Kudu 37,180, Kudu Maso Gabas 27,098

Hukumar Bayar da Lamunin Karatu ta Nijeriya (NELFund), ya raba jimillar kudade kimanin Naira biliyan 99.5 ga dalibai da cibiyoyin ilimi a cikin wata 16 kacal, tun bayan kaddamar da shirin bayar da rancen a ranar 24 ga Mayun 2024.

  • Manyan Jami’an Kasashen Afirka Suna Fatan Fadada Hadin Gwiwa Da Kasar Sin
  • Xi Ya Taya Jami’ar Tianjin Murnar Cika Shekaru 130 Da Kafuwa

Dangane da bayanan hukumar da LEADERSHIP ta samu daga rahoton matsayin rarraba lamunin daliban, wanda ke dauke da kwanan watan 24 ga Satumbar 2025, dalibai kimanin 510,378 ne ya zuwa yanzu suka ci gajiyar shirin bayar da rancen.

ADVERTISEMENT

Kasafin ya nuna cewa, an biya Naira biliyan 53.8 ne kai tsaye ga cibiyoyi ko makarantu a matsayin kudin karatu, yayin kuma da aka biya daliban Naira biliyan 45.7 a matsayin alawus-alawus.

Don haka, a dunkule dai; kimanin makarantu 228 ne ke cikin wannan tsari a halin yanzu a dukkanin fadin wannan kasa.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

Bayanan sun bayyana cewa; “Jimillar makarantu 228 suka ci gajiyar shirin, inda kimanin dalibai 829,423 suka nema. Ya zuwa yanzu kuma, dalibai 510,378 ne suka samu wannan tallafi na bayar da rance.

“Zuwa 10 ga watan Satumba, an biya kimanin Naira 53,801,717,293.00 a matsayin kudaden makaranta na daliban, yayin kuma da aka biya Naira 45,751,360,000.00 a matsayin alawus-alawus na daliban. Idan aka tattara kudaden baki-daya, jimillarsu ta kama Naira 99,553,077,293.00,” a cewar rahoton.

Duk da nasarar da aka samu a fadin kasar, shirin ya fuskanci kalubale wajen ganin an yi adalci a rabon a dukkanin shiyoyin fadin kasar guda shida da ake da su.

Alkaluman da LEADERSHIP ta tattara a watan Mayun 2025, sun nuna dimbin gibin da ke tsakanin Arewa da sauran yankunan fadin wannan kasa.

Arewa Maso Yamma, ta samu mafi yawan masu neman karatu da dalibai 157,831, sai kuma Arewa Maso Gabas da 127,058, haka nan kuma Kudu Maso Yamma da 92,850.

Akasin haka, dalibai 27,098 ne kadai daga Kudu Maso Gabas da kuma 37,180 daga Kudu Maso Kudu, yayin da Arewa ta Tsakiya ke da 74,120 da suka nema.

Yayin da aka yi kokarin jin karin bayani a kan rashin daidaiton da aka samu a fadin sassan kasar, Madam Oseyemi Oluwatuyi, Daraktar Sadarwa a Hukumar Bayar da Lamunin Karatu ta Nijeriya (NELFund), har yanzu ta ki cewa uffan, inda kadai ta ce; “A yi hakuri, ba za mu iya ba da irin wadannan bayanan ba, domin suna da matukar muhimmanci.”

Babu shakka, wadannan alkaluma; sun haifar da cece-kuce da kuma mabanbantan ra’ayoyi a tsakanin masu ruwa tsaki a harkar ilimi da kuma shugabannin yankuna.

Da yake zantawa da daya daga cikin wakilanmu, Mista Isaac Oche, masanin kididdiga da ke Abuja ya ce; karancin neman tallafin daga Jihohin Kudu Maso Gabas kamar yadda Hukumar Asusun Bayar da Lamunin Karatu ta Nijeriya (NELFund) ta rawaito a baya, na iya kasancewa ne sakamakon fargabar da daliban ke yin a gudun kada basussuka su yi musu yawa.

“Yawan adadin yana nuna cewa, dalibai daga Kudu bas u cika cin gajiyar wannan shiri ba, duk da cewa; na san Hukumar NELFUND, ta yi matukar taka-tsan-tsan a yankin, sannan kuma na yi imanin cewa; an samu ci gaba idan aka la’akari da halin da aka samu a halin yanzu,” in ji shi.

“Haka kuma, tana iya yiwuwa saboda rashin yarda da tsare-tsaren gwamnati ko kuma rashin sanin ya kamata tun daga tushe. Don haka, akwai bukatar wayar da kan jama’a na wannan yanki, sannan kuma ina yaba wa hukumar; bisa matukar kokarin da suka yi, amma har yanzu akwai bukatar a kara kaimi, domin kawar da shakku tare da aiwatar da gaskiya.”

A nasu bangaren, daliban sun yaba da shirin a matsayin daya daga cikin manufofin gwamnati mai ci a halin yanzu, amma kuma sun koka da yadda ta takaita alawus-alawus na wata-wata a lokacin hutu.

Cletus Tse, wanda dalibi ne na shekarar karshe, a Jami’ar Joseph Sarwuan Tarka da ke Makurdi, ya bayyana yadda tsarin ya kyautata tare da taimaka wa harkar iliminsa.

“Da ba dan wannan rance da aka ba mu ba, da tuni na ajiye wannan karatu tun a shekarata ta biyu, amma wannan taimako na kudi; ya taimaka min wajen mayar da hankali kan wannan karatu nawa, ba tare da fargabar yadda za a iya nemo kudin d azan biya kudin makaranta ba.”

Amma duk da haka, Tse, ya nuna damuwarsa dangane da yadda ake gudanar da tsarin rabon kudaden.

“ Ya kamata gwamnati ta yi kokarin ganin ta gaggauta biyan alawus-alawus din, saboda da dama daga cikinmu na fuskantar tsaiko wajen biyanmu, wani lokacin har sai zangon karatu ya kusa karewa, wanda hakan ya saba wa tsarin shirin,” in ji shi.

Tse ya kuma yi kira da a kara karfafa manufofin samar da ayyukan yi, domin tabbatar da ganin cewa; wadanda suka ci wannan bashi, sun samu damar biya a kan lokaci.

“Abu ne mai kyau ganin cewa, bashin yana taimaka mana wajen ci gaba da karatu, amma kuma biyan bashin zai iya tabbata ne kadai, idan da zarar mun kammala karatunmu; ya kasance aiki yana nan yana tsumayinmu.

Ya kara da cewa, “Dole ne gwamati ta daidaita wannan shirin da samar da ayyukan yi, don gukun kada kuma ya zama wani nauyi ko wani abu daban.

 

Rashin Aikin Yi Ne Babban Dalilin Da Ke Sare Wa Dalibai Gwiwa – Prof Obiaraeri

A nasa bangaren, tsohon dan takarar Sanata, kuma Farfesa a fannin shari’a, Farfesa Nnamdi Obiaraeri, ya dora laifin a kan rashin amfani da kafafen yada labarai wajen sanar da daliban da kuma matsalar rashin aiki ga wadanda suka kammala karatunsu.

Tsohon shugaban tsangayar shari’a na jami’ar Jihar Imo ya bayyana cewa, “Dalilan da suka hana da dama daga cikin dalibai neman wannan tallafi sun hada da rashin bin hanyoyin da suka dace wajen sanar da jama’a daga hukumar ta NELFUND. Wasu kalilan daga cikin makarantu ne suka tsaya tsayin daka wajen fadakar da dalibansu dangane da bayar da wannan rance tare kuma da nusasshe irin fa’idar da ke tattare da shi, musamman ga wadanda suke da karamin karfi ko rashin galihu.

 

Ba Mu Da Masaniya A Kan Bayar Da Wannan Lamuni- Wasu Iyaye Daga Abiya

Wani abin mamaki shi ne, wasu masu fada a ji a matakai daban-daban a Jihar Abiya, ba su san da batun bayar da lamunin ba.

Har ila yau, sun dora laifin a kan wani bangare na hukuma kan rashin wayar da kan jama’a game da wannan lamari da kuma su kansu daliban, ya kamata a ce sun san da wannan shiri; fiye ma da iyayen nasu ko kuma masu kula da su.

Wani fitaccen mamba a kungiyar al’adun kabilar Ibo, Libinus Nzedike, shi ma ya ce; rashin sanin ya kamata ne ko kuma kwarin gwiwa ya jawo haka.

Ya kara da cewa, “Tazarar da ke tsakanin Kudu Maso Gabas da Arewa Maso Yamma da kuma Kudu Maso Yamma, abu ne day a kamata a tsaya a duba yadda ya kamata, domin gano musabbabin faruwar hakan,” in ji shi.

Wani babban sakatare a daya daga cikin ma’aikatun, kuma fira-ministan gargajiya na al’ummar yankinsa, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya nuna rashin gamsuwa da yanayin matakin da yankin nasa ya dauka na rashin shiga shirin yadda ya kamata, su ma a dama da su.

Ya yi watsi da duk wani abin da aka ce, wanda ka iya haifar da wannan rashin shiga tsarin yadda ya kamata, domin ganin su ma an dama da su, yana mai cewa; hakan na iya faruwa sakamakon fargaba da juyayin tsawon lokacin da za a dauka na biya.

Wata shugabar mata a jam’iyyar APC (women leader), Nkechi Kanu, wadda ta yaba wa Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, bisa kokarin bullo da wannan shiri na bayar da lamuni, ta ce; daliban na cutar da kansu kwarai da gasket a hanyar kin shiga a dama da su yadda ya kamata.

Har ila yau, a karshe ta yi kira ga hukumomin gwamnati da shugabannin siyasa, al’umma, addini da kuma na gargajiya; das u hada kai wajen wayar da kan jama’a game da wannan asusu ko lamuni na gwamnatin tarayya a kowane lungu da sako na fadin wannan kasa.

Bashin
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Xi Da Takwaransa Na Singapore Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 35 Da Kulla Huldar Diflomasiyya

Xi Da Takwaransa Na Singapore Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 35 Da Kulla Huldar Diflomasiyya

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.