• English
  • Business News
Tuesday, August 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yanzu-Yanzu: Kotun Daukaka Kara Ta Sallami Nnamdi Kanu, Ta Kalubalanci Hukuncin Babbar Kotu 

by Sadiq
3 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Manyan Labarai
0
Yanzu-Yanzu: Kotun Daukaka Kara Ta Sallami Nnamdi Kanu, Ta Kalubalanci Hukuncin Babbar Kotu 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja ta sallami shugaban masu rajin fafutukar kafa kasar Biyafara, Nnamdi Kanu.

Gwamnatin Tarayya ta gurfanar da Kanu a gaban babbar kotun tarayya da ke Abuja bisa tuhume-tuhume 15 da suka shafi cin amanar kasa da ta’addanci, laifuffukan da ake zarginsa da aikatawa a yayin yakin neman zabensa.

  • An Yi Wa Manoma 5 Yankan Rago A Wani Sabon Rikici A Benuwe
  • 2023: Kuri’a Miliyan 95 Ce Za Ta Bayyana Wanda Zai Gaji Buhari – INEC

Wani kwamitin mutane uku da kotun daukaka kara, ya ce babbar kotun tarayya ba ta da hurumin yi masa shari’a bisa la’akari da yadda aka tsare shi da kuma yadda aka yi da shi wanda ya sabawa ka’ida.

Kotun ta ce tuhume-tuhume 15 da ake tuhumar Kanu ba a bayyana, kwanan wata, lokaci da kuma yanayin laifukan da ake zarginsa da aikatawa ba kafin a mika shi zuwa Nijeriya, wanda ya sabawa yarjejeniyar kasa da kasa.

Kotun ta ci gaba da cewa gwamnatin tarayya ta kasa bayyana inda aka kama Nnamdi Kanu duk da zarge-zargen da ake yi masa.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban ‘Yan Bindiga A Zamfara, Bello Turji, Ya Ajiye Makamai, Ya Saki Mutane 32

Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

An Zarge Shi Da Laifin Cin Amanar Kasa 

Mista Kanu ya sha yin kira da a balle wani yanki na kudancin Nijeriya domin kafa Jamhuriyar Biyafara.

A watan Oktoban 2015, hukumomin Nijeriya sun kama shi kan tuhume-tuhume 11 da suka hada da “ta’addanci, cin amanar kasa, jagorantar al’umma ba bisa ka’ida ba, buga labaran batanci, mallakar makamai ba bisa ka’ida ba da shigo da kaya ba bisa ka’ida ba, da sauransu.

“An bayar da belinsa ne a watan Afrilun 2017 saboda dalilai da suka shafi rashin lafiya.

“Sai dai Mista Kanu ya tsere daga kasar a watan Satumban 2017 bayan da sojoji suka mamaye gidansa da ke Afara-Ukwu, kusa da Umuahia a Jihar Abiya.

“Daga nan ne aka gan shi a Isra’ila, daga baya kuma ya ci gaba da tara magoya bayansa a Nijeriya don yin amfani da tashin hankali wajen samun ballewa.

“An zarge shi da laifin yin zagon kasa da ya hada da tada tarzoma ta hanyar talabijin da rediyo da watsa shirye-shirye ta yanar gizo a kan Nijeriya da jihohi da hukumomin Nijeriya,” in ji Ministan Shari’a, Abubakar Malami bayan an sake kama Kanu tare da dawo da shi Nijeriya a watan Yuni 2021.

“An kuma zargi Kanu da haddasa tashin hankali musamman a yankin Kudu maso Gabashin Nijeriya wanda ya yi sanadin asarar rayuka da dukiyoyin fararen hula, sojoji, jami’an ‘yansanda da lalata cibiyoyin farar hula da hukumomi.”

Mista Kanu ya musanta aikata laifikan da ake tuhumarsa da su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BiyafaraCin AmanaHukunciKanuKotuZargi
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Wa Manoma 5 Yankan Rago A Wani Sabon Rikici A Benuwe

Next Post

Ya Kamata Amurka Ta Koyi Darasi Daga Yakin Harajin Da Bai Yi Nasara Ba Kan Sin

Related

Shugaban ‘Yan Bindiga A Zamfara, Bello Turji, Ya Ajiye Makamai, Ya Saki Mutane 32
Manyan Labarai

Shugaban ‘Yan Bindiga A Zamfara, Bello Turji, Ya Ajiye Makamai, Ya Saki Mutane 32

58 minutes ago
Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

8 hours ago
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano
Manyan Labarai

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

1 day ago
Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 
Manyan Labarai

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

1 day ago
Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare
Manyan Labarai

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

2 days ago
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 
Da ɗumi-ɗuminsa

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

3 days ago
Next Post
Ya Kamata Amurka Ta Koyi Darasi Daga Yakin Harajin Da Bai Yi Nasara Ba Kan Sin

Ya Kamata Amurka Ta Koyi Darasi Daga Yakin Harajin Da Bai Yi Nasara Ba Kan Sin

LABARAI MASU NASABA

Shugaban ‘Yan Bindiga A Zamfara, Bello Turji, Ya Ajiye Makamai, Ya Saki Mutane 32

Shugaban ‘Yan Bindiga A Zamfara, Bello Turji, Ya Ajiye Makamai, Ya Saki Mutane 32

August 5, 2025
Xizang Ya Cimma Nasarorin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Suka Kafa Tarihi Cikin Shekaru Fiye Da 60

Xizang Ya Cimma Nasarorin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Suka Kafa Tarihi Cikin Shekaru Fiye Da 60

August 5, 2025
Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

August 5, 2025
Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida

Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida

August 5, 2025
LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya

LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya

August 5, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

August 5, 2025
Tsauraran Manufofin Tattalin Arziƙin Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

Tsauraran Manufofin Tattalin Arziƙin Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

August 5, 2025
BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

August 4, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

August 4, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.