• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NEDC Ta Raba Wa Mutanen Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa Kayan Abinci A Jihar Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Rahotonni
0
NEDC Ta Raba Wa Mutanen Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa Kayan Abinci A Jihar Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban daraktan gudanarwa na hukumar bunkasa shiyyar Arewa Maso Gabas (NEDC), Mohammed G. Alkali, ya nuna aniyar hukumar na yin hadin guiwar Gwamnatin jihar Bauchi domin labibo hanyoyin magance ambaliyar ruwa domin kiyaye barnar da hakan ka iya yi a nan gaba a fadin jihar.

Alhaji Mohammed G. Alkali ya yi bayanin cewa sun zo jihar Bauchi a ranar Laraba ne domin mika kyautar kayan abinci da wasu kayan bukatun yau da gobe ga wadanda ambaliyar ruwa ta shafa domin rage musu radadin halin da suke ciki a jihar ta Bauchi.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Abinci 4,200 Ga Marasa Karfi A Bauchi

Goni, ya kuma kara da jajanta wa gwamnati da al’ummar jihar bisa wannan ambaliyar ruwa da ta shafi jihar a bana da ya shafi wasu sassan jihar.

Ya yi bayanin kayan abinci da na sanyawa da suka bai wa jihar da cewa sun hada da buhunan shinkafa dubu 10 (10,000), bargunan rufuwa guda 5,000, atamfa na mata guda 5,000, shadda na maza guda 3,000, tabarma guda dubu biyar (5,000), galan din Mangeda guda 3,000, rigunan yara guda 3,000 da kuma dukka an mika su ga Gwamnatin jihar Bauchi da nufin rabawa ga wadanda lamarin ya shafa.

NEDC

Labarai Masu Nasaba

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa

MD, ya jinjina wa gwamnan Jihar Bauchi bisa kokarinsa na taimakawa ga wadanda ambaliyar ta shafa, ya yi fatan kayan abinci da wadanda ba na abincin da suka kawo jihar za su rage radadin tare da tallafawa ga wadanda ambaliyar ta shafa a jihar.

Alhaji Goni daga bisani ya yi magana kan ayyukan da hukumar ke gudanarwa a jihar Bauchi da suka hada da aikin hanyar Kirfi zuwa Gombe Abba, da ayyuka a sashin Ilimi, lafiya da sauran fannoni gami da saura da dama.

“Sannan, muna da aikin gina gidaje da ake ciki gaba da yi, sannan da aiki a daya daga cikin manyan cibiyoyin ilimi da na lafiya na jiha ko na tarayya, da kuma ayyukan su na cigaba da gudana.”

A nasa fannin, gwamna Bala Muhammad na Jihar, ya nuna matukar farin cikinsa bisa wannan tallafin da hukumar ta bai wa jihar, yana mai cewa samar da hukumar NEDC na daga cikin muhimman tarihi da nasarorin da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kafa a zamansa Shugaban kasa.

Ya ce, hukumar na daga cikin rassan da ke gudanar da ayyukansu da ke zuwa ga talakawa da al’umma kai tsaye, kuma sa a jima ana amfanuwa da ayyukan da suke gudanarwa.

Ya kuma jinjina kan yadda hukumar ke gudanar da ayyukanta na farfado da shiyyar Arewa Maso Gabas da hare-haren Boko Haram ya daidaiya a shekarun baya.

Gwamna Bala ya sanar da bakin nasa cewa tabbas ambaliyar ruwa ta yi barna sosai a jihar, ya nuna cewa hatta shi kansa da Gwamnatinsa sun yi kokarin samar da tallafin gaggawa ga wadanda lamarin ya shafa, ya nuna cewa lamarin ne ya yi yawa sosai amma sun yi kokari sosai wajen samar da nasu tallafin a matakin jihar.

NEDC

Kan hakan ne ya nuna cewa kayan tallafin abinci da na wadanda ba abinci ba da suka samu daga hukumar za su taimaka sosai ga wadanda ambaliyar ta shafa.

Kana, ya jinjina da ayyukan da hukumar ke gudanarwa a jihar da cewa tabbas hakan na taimaka wa rayuwar al’ummar jihar.

Daga bisani ne kuma MD, Alkali ya mika kayan tallafin da suka kawo jihar ta hannun mataimakin gwamnan Jihar Bauchi Sanata Baba Tela da nufin rabawa ga wadanda lamarin ya shafa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dan Chinan Da Ake Zargi Da Kisan Budurwarsa ‘Ummita’ A Kano Ya Musanta Aikata Kisan

Next Post

Xi Ya Jagoranci Shugabannin JKS Zuwa Tsohuwar Hedkwatar Jam’iyyar  

Related

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari
Rahotonni

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

11 hours ago
Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa
Rahotonni

Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa

1 week ago
Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya
Rahotonni

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

1 week ago
Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda
Rahotonni

Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda

1 week ago
Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

4 weeks ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

4 weeks ago
Next Post
Xi Ya Jagoranci Shugabannin JKS Zuwa Tsohuwar Hedkwatar Jam’iyyar  

Xi Ya Jagoranci Shugabannin JKS Zuwa Tsohuwar Hedkwatar Jam’iyyar  

LABARAI MASU NASABA

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.