ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NEDC Ta Raba Wa Mutanen Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa Kayan Abinci A Jihar Bauchi

by Khalid Idris Doya
4 years ago
NEDC

Babban daraktan gudanarwa na hukumar bunkasa shiyyar Arewa Maso Gabas (NEDC), Mohammed G. Alkali, ya nuna aniyar hukumar na yin hadin guiwar Gwamnatin jihar Bauchi domin labibo hanyoyin magance ambaliyar ruwa domin kiyaye barnar da hakan ka iya yi a nan gaba a fadin jihar.

Alhaji Mohammed G. Alkali ya yi bayanin cewa sun zo jihar Bauchi a ranar Laraba ne domin mika kyautar kayan abinci da wasu kayan bukatun yau da gobe ga wadanda ambaliyar ruwa ta shafa domin rage musu radadin halin da suke ciki a jihar ta Bauchi.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Abinci 4,200 Ga Marasa Karfi A Bauchi

Goni, ya kuma kara da jajanta wa gwamnati da al’ummar jihar bisa wannan ambaliyar ruwa da ta shafi jihar a bana da ya shafi wasu sassan jihar.

ADVERTISEMENT

Ya yi bayanin kayan abinci da na sanyawa da suka bai wa jihar da cewa sun hada da buhunan shinkafa dubu 10 (10,000), bargunan rufuwa guda 5,000, atamfa na mata guda 5,000, shadda na maza guda 3,000, tabarma guda dubu biyar (5,000), galan din Mangeda guda 3,000, rigunan yara guda 3,000 da kuma dukka an mika su ga Gwamnatin jihar Bauchi da nufin rabawa ga wadanda lamarin ya shafa.

NEDC

LABARAI MASU NASABA

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

MD, ya jinjina wa gwamnan Jihar Bauchi bisa kokarinsa na taimakawa ga wadanda ambaliyar ta shafa, ya yi fatan kayan abinci da wadanda ba na abincin da suka kawo jihar za su rage radadin tare da tallafawa ga wadanda ambaliyar ta shafa a jihar.

Alhaji Goni daga bisani ya yi magana kan ayyukan da hukumar ke gudanarwa a jihar Bauchi da suka hada da aikin hanyar Kirfi zuwa Gombe Abba, da ayyuka a sashin Ilimi, lafiya da sauran fannoni gami da saura da dama.

“Sannan, muna da aikin gina gidaje da ake ciki gaba da yi, sannan da aiki a daya daga cikin manyan cibiyoyin ilimi da na lafiya na jiha ko na tarayya, da kuma ayyukan su na cigaba da gudana.”

A nasa fannin, gwamna Bala Muhammad na Jihar, ya nuna matukar farin cikinsa bisa wannan tallafin da hukumar ta bai wa jihar, yana mai cewa samar da hukumar NEDC na daga cikin muhimman tarihi da nasarorin da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kafa a zamansa Shugaban kasa.

Ya ce, hukumar na daga cikin rassan da ke gudanar da ayyukansu da ke zuwa ga talakawa da al’umma kai tsaye, kuma sa a jima ana amfanuwa da ayyukan da suke gudanarwa.

Ya kuma jinjina kan yadda hukumar ke gudanar da ayyukanta na farfado da shiyyar Arewa Maso Gabas da hare-haren Boko Haram ya daidaiya a shekarun baya.

Gwamna Bala ya sanar da bakin nasa cewa tabbas ambaliyar ruwa ta yi barna sosai a jihar, ya nuna cewa hatta shi kansa da Gwamnatinsa sun yi kokarin samar da tallafin gaggawa ga wadanda lamarin ya shafa, ya nuna cewa lamarin ne ya yi yawa sosai amma sun yi kokari sosai wajen samar da nasu tallafin a matakin jihar.

NEDC

Kan hakan ne ya nuna cewa kayan tallafin abinci da na wadanda ba abinci ba da suka samu daga hukumar za su taimaka sosai ga wadanda ambaliyar ta shafa.

Kana, ya jinjina da ayyukan da hukumar ke gudanarwa a jihar da cewa tabbas hakan na taimaka wa rayuwar al’ummar jihar.

Daga bisani ne kuma MD, Alkali ya mika kayan tallafin da suka kawo jihar ta hannun mataimakin gwamnan Jihar Bauchi Sanata Baba Tela da nufin rabawa ga wadanda lamarin ya shafa.

NEDC
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

NEDC
Rahotonni

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

May 17, 2026
NEDC
Rahotonni

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Rahotonni

Almajiranci:Matsala Ko Maslaha

May 10, 2026
Next Post
Xi Ya Jagoranci Shugabannin JKS Zuwa Tsohuwar Hedkwatar Jam’iyyar  

Xi Ya Jagoranci Shugabannin JKS Zuwa Tsohuwar Hedkwatar Jam’iyyar  

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.