• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwastam Ta Kama Kayan Fasa Kwauri Da Kudinsu Ya Kai Miliyan 78.6 A Kebbi

by Umar Faruk
3 years ago
in Labarai
0
Kwastam Ta Kama Kayan Fasa Kwauri Da Kudinsu Ya Kai Miliyan 78.6 A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Hana Fasa Kwauri ta Kasa (NCS) a Jihar Kebbi, ta kama wasu kayayyakin fasa kwauri da kudinsu ya kai Naira miliyan 78.6 a watan Oktoban 2022 a jihar.

Shugaban hukumar Kwastam, Mista Joseph Attah ne ya bayyana haka a lokacin da ya ke zantawa da manema labarai a kan ayyukan hukumar na watan Oktoba a Birnin Kebbi.

  • Shugaba Xi Zai Gabatar Da Jawabi A Yayin Bude Baje Kolin CIIE Karo Na 5
  • Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Samar Da Fa’ida A Zahiri Ga Jama’ar Afirka

Ya ce rundunar ta samu nasarori a cikin muhimman ayyukan da suka shafi aikin dakile fasa kwauri, ta samar da kudaden shiga da kuma saukaka kasuwanci.

A cewarsa: “An ci gaba da samun karuwar kudaden shiga na hukumar. A tsawon lokacin da ake bitar, mun samar da zunzurutun kudi har Naira miliyan 162.2 a matsayin kudaden shiga daga harajin shigo da kayayyaki. Wannan shi ne mafi girma tun bayan bude iyakar ta Kamba da ke a Jihar ta Kebbi.

“Rundunar ta kuma taimaka wajen fitar da kayayyakin da ake sarrafa su a cikin gida na sama da Naira biliyan 2 a daidai lokacin da ake gudanar da bincike,” in ji Attah.

Labarai Masu Nasaba

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ya ce, rundunar ta umurci jami’ansu da su kara sanya ido a cikin lungu da sako na lungu da sako na ruwa a kokarinsu na dakile ayyukan fasa-kwauri a cikin lungu da sako na jihar.

“Saboda haka, kokarin da aka yi ya haifar da kama wasu kayayyaki iri-iri har 16 da suka hada da, fakiti 284 na kwamfutar tafi-da-gidanka, tabar wi-wi, motoci 4 da aka yi amfani da su, wadanda kuma akwai Motocin na shi ga jama’a kirar Honda guda biyu da aka yi amfani da su, da motar dizal guda daya da kuma babbar motar tifa.

“Sauran sun hada da, bale 139 na tufafin hannu, buhunan shinkafa 345 na kasar waje (kowanne kilogiram 50), lita 2,250 na man fetur (PMS), kwali 38 na man shafawa (bleaching cream), guda 80 na batura masu amfani da hasken rana, da dai sauransu.

“Abin da ake tsamani da za a biya na harajin kayayyakin da aka kama ya kai Naira miliyan 78.6,” inji shi.

Kazalika, Mista Attah ya bayyana kudurin rundunar na tabbatar da cewa wadanda suka zabi shigo da kaya ko fitar da su ta iyakar Kamba, sai bin ka’idojin da suka dace na dokar kasa.

“Za ku yarda da ni, cewa yayin da sauran kayayyakin da aka kama na da kididdigar kudi, ba za mu iya kididdige yawan barnar da kwayoyi masu hadari da sauran abubuwa ke haifarwa a cikin al’umma ba.”

Bugu da kari ya ce “Irin wannan abu idan aka fito da shi a cikin al’umma yana taimaka wa dukkan manyan laifukan da muke gani a cikin al’ummarmu.

“Za a mika tabar wi-wi ga hukumar NDLEA jihar Kebbi domin daukar matakin da ya dace,” in ji shi.

Daga karshe dai, mista Joseph Attah ya tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da gudanar da aikin da aka ba su na dakile ayyukan fasa kwaurin ba tare da kasawa ba duk da kalubalen da ake fuskanta daga ‘yan kasa masu taimaka wa ga aikata miyagun laifuka a kan jami’ansu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hukumar Hana Fasa KwauriKayayyakiKebbiMiliyoyin Kudi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaba Xi Zai Gabatar Da Jawabi A Yayin Bude Baje Kolin CIIE Karo Na 5

Next Post

An Kashe ‘Yan Bindiga A Kasuwa A Zamafara

Related

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya
Labarai

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

1 hour ago
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi
Labarai

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

2 hours ago
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa
Labarai

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

2 hours ago
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba
Labarai

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

3 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

6 hours ago
Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 
Labarai

Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

6 hours ago
Next Post
An Kashe ‘Yan Bindiga A Kasuwa A Zamafara

An Kashe 'Yan Bindiga A Kasuwa A Zamafara

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.