ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoman Alkama 200 Za Su Amfana Da Shirin NALDA A Jihar Jigawa

by Munkaila T. Abdullahi
3 years ago
Alkama

Kimanin manoman alkama 200 ne wadanda suka fito daga sassa daban-daban na Jihar Jigawa za su amfana da shirin NALDA a noman rani na wannan shekara ta 2022.

Jagoran NALDA a Jihar Jigawa, Malam Bello Umar ne ya bayyana haka a yayin taron wayar da kan manoma a kan shirin na NALDA wadda ya gudana ranar Litinin da ta gabata a garin Kazaure.

  • Yadda BBC Hausa Ya Karrama Gwarazan Gasar Waƙa Da Hikayata Ta Bana
  • Sin Ta Sanar Da Shirin Bunkasa Fasahar VR

Malam Umar ya ce duba da yadda Allah ya albarkaci jihar da kasar noma ya sa NALDA ta zabi garin Marke karkashin karamar hukumar Kaugama a shekarar da ta gabata da kuma yankin Gumuna-Gora a Kazaure a noman rani na wannan shekara ta 2022.

ADVERTISEMENT

Jagoran wadda ya ce tuni shirye-shirye sun yi nisa, ya ce tuni manoman sun fara gyare-gyaren gonakinsu da kaftu domin fara aikin alkamar wadda nan ba da dadewa ba za a raba musu sauran kayayyakin.

Ya karawa cewa kayayyakin sun hada da magunguna da injin feshi da ingantaccen iri da takin zamani da injin ban ruwa da injin girbin amfanin gona tare da ba su tabbacin ingantaccen farashi idan Allah ya yi amfanin.

LABARAI MASU NASABA

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

“A shekarar 2020, an yi wa wannan shiri lakabi da taken ‘A dama da kowa’ wadda ya mayar da hankali wajen magance barazanar yunwa a duniya baki daya.

“Duba da har zuwa yanzu akwai barazanar karancin abinci sakamakon kalubalan annoba da kuma canjin yanayi ya sa taken shirin a wannan shekarar ya maida hankali wajen kira ga kungiyoyin manoma da sauran manyan manoma su yi amfani da sabbin dabarun noma na zamani domin cimma nasarar samar da wadataccen abinci saboda magance yunwa a duniya baki daya.

A yayin taron bitar an gabatar da mukaloli da suka shafi noman alkama tare da kara wa juna sani tsakanin manoma matasa da mata Manoma.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Noma Da Kiwo

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi
Noma Da Kiwo

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Next Post
Sin: Abubuwan Dake Cikin Rahoton Tsaron Amurka Na 2022 Game Da Sin Tsohon Tunani Ne Na Yakin Cacar Baka

Sin: Abubuwan Dake Cikin Rahoton Tsaron Amurka Na 2022 Game Da Sin Tsohon Tunani Ne Na Yakin Cacar Baka

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

November 14, 2025
ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

November 14, 2025

Rikicin PDP: Fiye Da Wakilai 3,000 Ne Za Su Raba Gardama A Babban Taron Jam’iyyar

November 14, 2025
Kasar Sin Ta Kara Azamar Kirkiro Da Fasahar Sadarwar 6G

Kasar Sin Ta Kara Azamar Kirkiro Da Fasahar Sadarwar 6G

November 14, 2025
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

November 14, 2025
Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne

Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne

November 14, 2025
Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

November 14, 2025
Manzon Allah (SAW) A Matsayin Dan Gatan Allah 

Manzon Allah (SAW) A Matsayin Dan Gatan Allah 

November 14, 2025
Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma: Martani

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma: Martani

November 14, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe

Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.