• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yin Amfani Da Yanar Gizo Wajen Raya Duniya

by CMG Hausa
3 years ago
Duniya

Abokaina, ko kun taba zuwa kauyen Tobolo na jihar Ogun? A can za ku iya ganin yadda yanar gizo ta Internet, da sauran fasahohin sadarwa na zamani suke haifar da sauye-sauye ga zaman rayuwar mutane.

Ko da yake babu wutar lantarki a kauyen Tobolo, amma ya samu turken sadarwar wayar salula na kansa. Mutanen kauyen suna kiran wannan turken sadarwa, da wani kamfanin Sin ya kafa shi, da taken “sanda”, saboda ba shi da girma. Amma duk da haka, na’urar na da inganci: Tana aiki ne bisa yin amfani da zafin rana, kana layin da ta samar ya shafi kauyen Tobolo da sauran kauyuka makwabtansa. Idan ana ruwan sama, ko babu rana, wannan turke na iya ci gaba da aikin har tsawon sa’o’i 48.

  • Gina Al’umma Mai Makoma Ta Bai Daya A Kafar Intanet Na Da Muhimmanci A Zamanin Da Ake Ciki

Kafin a samu layi, mutanen kauyen Tobolo su kan hau itace don buga waya. Saboda a can sama ana iya samun layi na kasar Benin. Sai dai kudin layin yana da tsada, kana a kan samu matsalar katsewar layin, ga kuma wahalar hawa itace.

Zuwa yanzu, mutanen kauyen suna iya yin amfani da wayar salula wajen tuntubar abokai cikin matukar sauki. Shago na chajin waya ya samu karin kasuwanci sosai, ganin yadda kashi 80% na mazauna kauyen suka fara yin amfani da wayar salula. Ban da wannan kuma, wasu sabbin kantuna sun fara aiki bi da bi a cikin kauyen, bisa yadda mutanen kauyen suke samun bayanan kasuwanci a kai a kai ta wayar salula.

Labarin kauyen Tobolo wani misali ne game da yadda kasar Sin da kasashen Afirka suke kokarin aiwatar da shawarar kafa al’umma mai makomar bai daya a fannin yanar gizo ta Internet da fasahohin sadarwa, wanda kasar Sin ta gabatar. Wadda ta shafi hadin gwiwa don gina kayayyakin more rayuwa ta fuskar aikin sadarwa, da ba da taimako ga mutane masu karamin karfi, da dai sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

Sai dai me ya sa kasar Sin ta ba da shawarar kafa wata al’umma mai makomar bai daya ta bangaren yanar gizo ta Internet a duniya? Dalilin shi ne neman daidaita wasu matsalolin da ake fuskanta a yanzu, inda wasu kasashe ke son yin amfani da fifikonsu a fannin kimiyya da fasaha, wajen kokarin mai da yanar gizo ta Internet wani makami, ta yadda za su iya kiyaye matsayinsu na yin babakere a duniya. Ko da yake fasahar yanar gizo fasaha ce ta zamani, amma suna neman yin amfani da ita don aiwatar da tsohon tunani na kashin dankali.

Abun tambaya a nan shi ne, da yin amfani da fasahar yanar gizo wajen yin babakere a duniya, da kuma yin amfani da ita wajen kyautata zaman rayuwar dan Adam, wane ne ya fi dacewa? Na san amsar hakan na cikin zuciyar kowa. (Bello Wang)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona
Daga Birnin Sin

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Next Post
Kamfanin Sin Ya Haskaka Kauyen Lauteye Na Jihar Kanon Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Haskaka Kauyen Lauteye Na Jihar Kanon Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.