ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yin Amfani Da Yanar Gizo Wajen Raya Duniya

by CMG Hausa
4 years ago
Duniya

Abokaina, ko kun taba zuwa kauyen Tobolo na jihar Ogun? A can za ku iya ganin yadda yanar gizo ta Internet, da sauran fasahohin sadarwa na zamani suke haifar da sauye-sauye ga zaman rayuwar mutane.

Ko da yake babu wutar lantarki a kauyen Tobolo, amma ya samu turken sadarwar wayar salula na kansa. Mutanen kauyen suna kiran wannan turken sadarwa, da wani kamfanin Sin ya kafa shi, da taken “sanda”, saboda ba shi da girma. Amma duk da haka, na’urar na da inganci: Tana aiki ne bisa yin amfani da zafin rana, kana layin da ta samar ya shafi kauyen Tobolo da sauran kauyuka makwabtansa. Idan ana ruwan sama, ko babu rana, wannan turke na iya ci gaba da aikin har tsawon sa’o’i 48.

  • Gina Al’umma Mai Makoma Ta Bai Daya A Kafar Intanet Na Da Muhimmanci A Zamanin Da Ake Ciki

Kafin a samu layi, mutanen kauyen Tobolo su kan hau itace don buga waya. Saboda a can sama ana iya samun layi na kasar Benin. Sai dai kudin layin yana da tsada, kana a kan samu matsalar katsewar layin, ga kuma wahalar hawa itace.

ADVERTISEMENT

Zuwa yanzu, mutanen kauyen suna iya yin amfani da wayar salula wajen tuntubar abokai cikin matukar sauki. Shago na chajin waya ya samu karin kasuwanci sosai, ganin yadda kashi 80% na mazauna kauyen suka fara yin amfani da wayar salula. Ban da wannan kuma, wasu sabbin kantuna sun fara aiki bi da bi a cikin kauyen, bisa yadda mutanen kauyen suke samun bayanan kasuwanci a kai a kai ta wayar salula.

Labarin kauyen Tobolo wani misali ne game da yadda kasar Sin da kasashen Afirka suke kokarin aiwatar da shawarar kafa al’umma mai makomar bai daya a fannin yanar gizo ta Internet da fasahohin sadarwa, wanda kasar Sin ta gabatar. Wadda ta shafi hadin gwiwa don gina kayayyakin more rayuwa ta fuskar aikin sadarwa, da ba da taimako ga mutane masu karamin karfi, da dai sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

Sai dai me ya sa kasar Sin ta ba da shawarar kafa wata al’umma mai makomar bai daya ta bangaren yanar gizo ta Internet a duniya? Dalilin shi ne neman daidaita wasu matsalolin da ake fuskanta a yanzu, inda wasu kasashe ke son yin amfani da fifikonsu a fannin kimiyya da fasaha, wajen kokarin mai da yanar gizo ta Internet wani makami, ta yadda za su iya kiyaye matsayinsu na yin babakere a duniya. Ko da yake fasahar yanar gizo fasaha ce ta zamani, amma suna neman yin amfani da ita don aiwatar da tsohon tunani na kashin dankali.

Abun tambaya a nan shi ne, da yin amfani da fasahar yanar gizo wajen yin babakere a duniya, da kuma yin amfani da ita wajen kyautata zaman rayuwar dan Adam, wane ne ya fi dacewa? Na san amsar hakan na cikin zuciyar kowa. (Bello Wang)

 

Duniya
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
Daga Birnin Sin

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Next Post
Kamfanin Sin Ya Haskaka Kauyen Lauteye Na Jihar Kanon Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Haskaka Kauyen Lauteye Na Jihar Kanon Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.