• Leadership Hausa
Saturday, March 25, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yin Amfani Da Yanar Gizo Wajen Raya Duniya

by CMG Hausa
5 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Yin Amfani Da Yanar Gizo Wajen Raya Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Abokaina, ko kun taba zuwa kauyen Tobolo na jihar Ogun? A can za ku iya ganin yadda yanar gizo ta Internet, da sauran fasahohin sadarwa na zamani suke haifar da sauye-sauye ga zaman rayuwar mutane.

Ko da yake babu wutar lantarki a kauyen Tobolo, amma ya samu turken sadarwar wayar salula na kansa. Mutanen kauyen suna kiran wannan turken sadarwa, da wani kamfanin Sin ya kafa shi, da taken “sanda”, saboda ba shi da girma. Amma duk da haka, na’urar na da inganci: Tana aiki ne bisa yin amfani da zafin rana, kana layin da ta samar ya shafi kauyen Tobolo da sauran kauyuka makwabtansa. Idan ana ruwan sama, ko babu rana, wannan turke na iya ci gaba da aikin har tsawon sa’o’i 48.

  • Gina Al’umma Mai Makoma Ta Bai Daya A Kafar Intanet Na Da Muhimmanci A Zamanin Da Ake Ciki

Kafin a samu layi, mutanen kauyen Tobolo su kan hau itace don buga waya. Saboda a can sama ana iya samun layi na kasar Benin. Sai dai kudin layin yana da tsada, kana a kan samu matsalar katsewar layin, ga kuma wahalar hawa itace.

Zuwa yanzu, mutanen kauyen suna iya yin amfani da wayar salula wajen tuntubar abokai cikin matukar sauki. Shago na chajin waya ya samu karin kasuwanci sosai, ganin yadda kashi 80% na mazauna kauyen suka fara yin amfani da wayar salula. Ban da wannan kuma, wasu sabbin kantuna sun fara aiki bi da bi a cikin kauyen, bisa yadda mutanen kauyen suke samun bayanan kasuwanci a kai a kai ta wayar salula.

Labarin kauyen Tobolo wani misali ne game da yadda kasar Sin da kasashen Afirka suke kokarin aiwatar da shawarar kafa al’umma mai makomar bai daya a fannin yanar gizo ta Internet da fasahohin sadarwa, wanda kasar Sin ta gabatar. Wadda ta shafi hadin gwiwa don gina kayayyakin more rayuwa ta fuskar aikin sadarwa, da ba da taimako ga mutane masu karamin karfi, da dai sauransu.

Labarai Masu Nasaba

An Bude Dandalin Tattauna Harkokin Samar Da Ci Gaba Na Kasar Sin

Rukunin Na’urori Na Biyar Na Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta “Lower Kefu Gorge” Dake Zambiya Sun Fara Aiki

Sai dai me ya sa kasar Sin ta ba da shawarar kafa wata al’umma mai makomar bai daya ta bangaren yanar gizo ta Internet a duniya? Dalilin shi ne neman daidaita wasu matsalolin da ake fuskanta a yanzu, inda wasu kasashe ke son yin amfani da fifikonsu a fannin kimiyya da fasaha, wajen kokarin mai da yanar gizo ta Internet wani makami, ta yadda za su iya kiyaye matsayinsu na yin babakere a duniya. Ko da yake fasahar yanar gizo fasaha ce ta zamani, amma suna neman yin amfani da ita don aiwatar da tsohon tunani na kashin dankali.

Abun tambaya a nan shi ne, da yin amfani da fasahar yanar gizo wajen yin babakere a duniya, da kuma yin amfani da ita wajen kyautata zaman rayuwar dan Adam, wane ne ya fi dacewa? Na san amsar hakan na cikin zuciyar kowa. (Bello Wang)

 

ShareTweetSendShare
Previous Post

El-Rufai Ya Bayar Da Umarnin Mayar Wa Dalibai Kudadensu Na Makaranta Da Aka Karba

Next Post

Kamfanin Sin Ya Haskaka Kauyen Lauteye Na Jihar Kanon Nijeriya

Related

An Bude Dandalin Tattauna Harkokin Samar Da Ci Gaba Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Bude Dandalin Tattauna Harkokin Samar Da Ci Gaba Na Kasar Sin

3 mins ago
Rukunin Na’urori Na Biyar Na Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta “Lower Kefu Gorge” Dake Zambiya Sun Fara Aiki
Daga Birnin Sin

Rukunin Na’urori Na Biyar Na Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta “Lower Kefu Gorge” Dake Zambiya Sun Fara Aiki

1 hour ago
An Yi Zaman Taron “Kare Hakkin ‘Yan Kananan Kabilu A Sabon Zamani” A Geneva
Daga Birnin Sin

An Yi Zaman Taron “Kare Hakkin ‘Yan Kananan Kabilu A Sabon Zamani” A Geneva

1 hour ago
Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Daina Muzgunawa Kamfanonin Waje
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Daina Muzgunawa Kamfanonin Waje

19 hours ago
Kamata Ya Yi Amurka Ta Nemi Amincewa Daga Kasa Da Kasa Kafin Komawar Ta Hukumar UNESCO
Daga Birnin Sin

Kamata Ya Yi Amurka Ta Nemi Amincewa Daga Kasa Da Kasa Kafin Komawar Ta Hukumar UNESCO

20 hours ago
CMG Ta Hada Kai Da Manyan Kafafen Yada Labaran Kasashen Afirka Biyar Don Kaddamar Da Wani Shirin TV Mai Suna “More Ci Gaba Tare”
Daga Birnin Sin

CMG Ta Hada Kai Da Manyan Kafafen Yada Labaran Kasashen Afirka Biyar Don Kaddamar Da Wani Shirin TV Mai Suna “More Ci Gaba Tare”

22 hours ago
Next Post
Kamfanin Sin Ya Haskaka Kauyen Lauteye Na Jihar Kanon Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Haskaka Kauyen Lauteye Na Jihar Kanon Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

An Bude Dandalin Tattauna Harkokin Samar Da Ci Gaba Na Kasar Sin

An Bude Dandalin Tattauna Harkokin Samar Da Ci Gaba Na Kasar Sin

March 25, 2023
Burina Masu Basira Su Rika Amfana Da Basirarsu -Haidar Blog

Burina Masu Basira Su Rika Amfana Da Basirarsu -Haidar Blog

March 25, 2023
Rukunin Na’urori Na Biyar Na Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta “Lower Kefu Gorge” Dake Zambiya Sun Fara Aiki

Rukunin Na’urori Na Biyar Na Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta “Lower Kefu Gorge” Dake Zambiya Sun Fara Aiki

March 25, 2023
An Yi Zaman Taron “Kare Hakkin ‘Yan Kananan Kabilu A Sabon Zamani” A Geneva

An Yi Zaman Taron “Kare Hakkin ‘Yan Kananan Kabilu A Sabon Zamani” A Geneva

March 25, 2023
Ra’ayoyin Jam’iyyu Kan Nassarar Abba A Kano

Ra’ayoyin Jam’iyyu Kan Nassarar Abba A Kano

March 25, 2023
Tarihin Zaben Kano: Hannun Karba, Hannun Mayarwa

Tarihin Zaben Kano: Hannun Karba, Hannun Mayarwa

March 25, 2023
Falalar Ramadan Da Wasu Hukunce-hukuncen Azumi

Falalar Ramadan Da Wasu Hukunce-hukuncen Azumi

March 25, 2023
Muna Samun Tallafi Daga Sarkin Noman Masarautar Gaya – Kungiyar Manoman

Muna Samun Tallafi Daga Sarkin Noman Masarautar Gaya – Kungiyar Manoman

March 25, 2023
Matsayin Da Dimukradiyyar Nijeriya Ta Kai A Yanzu – Buhari

Matsayin Da Dimukradiyyar Nijeriya Ta Kai A Yanzu – Buhari

March 25, 2023
INEC Ta Yi Mun Daidai Da Ta Ayyana Zaɓen Gwamnan Adamawa Bai Kammalu Ba – Binani

INEC Ta Yi Mun Daidai Da Ta Ayyana Zaɓen Gwamnan Adamawa Bai Kammalu Ba – Binani

March 25, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.