ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yin Amfani Da Yanar Gizo Wajen Raya Duniya

by CMG Hausa
4 years ago
Duniya

Abokaina, ko kun taba zuwa kauyen Tobolo na jihar Ogun? A can za ku iya ganin yadda yanar gizo ta Internet, da sauran fasahohin sadarwa na zamani suke haifar da sauye-sauye ga zaman rayuwar mutane.

Ko da yake babu wutar lantarki a kauyen Tobolo, amma ya samu turken sadarwar wayar salula na kansa. Mutanen kauyen suna kiran wannan turken sadarwa, da wani kamfanin Sin ya kafa shi, da taken “sanda”, saboda ba shi da girma. Amma duk da haka, na’urar na da inganci: Tana aiki ne bisa yin amfani da zafin rana, kana layin da ta samar ya shafi kauyen Tobolo da sauran kauyuka makwabtansa. Idan ana ruwan sama, ko babu rana, wannan turke na iya ci gaba da aikin har tsawon sa’o’i 48.

  • Gina Al’umma Mai Makoma Ta Bai Daya A Kafar Intanet Na Da Muhimmanci A Zamanin Da Ake Ciki

Kafin a samu layi, mutanen kauyen Tobolo su kan hau itace don buga waya. Saboda a can sama ana iya samun layi na kasar Benin. Sai dai kudin layin yana da tsada, kana a kan samu matsalar katsewar layin, ga kuma wahalar hawa itace.

ADVERTISEMENT

Zuwa yanzu, mutanen kauyen suna iya yin amfani da wayar salula wajen tuntubar abokai cikin matukar sauki. Shago na chajin waya ya samu karin kasuwanci sosai, ganin yadda kashi 80% na mazauna kauyen suka fara yin amfani da wayar salula. Ban da wannan kuma, wasu sabbin kantuna sun fara aiki bi da bi a cikin kauyen, bisa yadda mutanen kauyen suke samun bayanan kasuwanci a kai a kai ta wayar salula.

Labarin kauyen Tobolo wani misali ne game da yadda kasar Sin da kasashen Afirka suke kokarin aiwatar da shawarar kafa al’umma mai makomar bai daya a fannin yanar gizo ta Internet da fasahohin sadarwa, wanda kasar Sin ta gabatar. Wadda ta shafi hadin gwiwa don gina kayayyakin more rayuwa ta fuskar aikin sadarwa, da ba da taimako ga mutane masu karamin karfi, da dai sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Sai dai me ya sa kasar Sin ta ba da shawarar kafa wata al’umma mai makomar bai daya ta bangaren yanar gizo ta Internet a duniya? Dalilin shi ne neman daidaita wasu matsalolin da ake fuskanta a yanzu, inda wasu kasashe ke son yin amfani da fifikonsu a fannin kimiyya da fasaha, wajen kokarin mai da yanar gizo ta Internet wani makami, ta yadda za su iya kiyaye matsayinsu na yin babakere a duniya. Ko da yake fasahar yanar gizo fasaha ce ta zamani, amma suna neman yin amfani da ita don aiwatar da tsohon tunani na kashin dankali.

Abun tambaya a nan shi ne, da yin amfani da fasahar yanar gizo wajen yin babakere a duniya, da kuma yin amfani da ita wajen kyautata zaman rayuwar dan Adam, wane ne ya fi dacewa? Na san amsar hakan na cikin zuciyar kowa. (Bello Wang)

 

Duniya
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Kamfanin Sin Ya Haskaka Kauyen Lauteye Na Jihar Kanon Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Haskaka Kauyen Lauteye Na Jihar Kanon Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.