• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata A Binciki Bankin Raya Kasa Da Gwamnati Ta Kafa – Ndume

by yahuzajere
3 years ago
in Labarai
0
Ya Kamata A Binciki Bankin Raya Kasa Da Gwamnati Ta Kafa – Ndume
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kwamitin Rundunar Soji a Majalisar Dattawa, Sanata Muhammad Ndume ya bayyana cewa akwai bukatar a binciki Bankin Ci Gaban Nijeriya watau Development Bank of Nigeria (DBN) da Gwamnatin Tarayya ta kafa domin taimakawa kananan masana’antu da `yan Kasuwa sakamakon zargin gudanar da al’amura ta hanyar da bata dace ba.

  • Buhari Ya Halarci Wajen Kaddamar Da Hako Man Fetur A Bauchi 

Ndume wanda ya kasance mamba a cikin wani kwamitin na wucin gadi na mutane bakwai da Sanata Muhammad Sani Musa 313 ke jagoranta a Majalisar Dattawan Tarayyar, ya yi nuni da cewa a wani binciken da suka yi alamu na nuni da cewa kwalliya ba ta biya kuɗin sabulu ba.

Ya kara da cewa an kawo Kudirin Dokar ne domin a binciki Bankin ta DBN wanda Gwamnatin Tarayya ta kafa saboda tabbatar da an taimaka wa kananan `yan Kasuwa da masana’antu domin su samu tallafi mai sauki ta yadda za su farfado ko su kafa kananan masana’antu wanda yake da mahimmaci ga masu kananan karfi domin idan aka farfado da wannan `yan Kasuwa da masana’antu shi ne za a iya farfado da tattalin Arzikin Kasar.

Ya ce “amma abun takaici shi ne mun lura a cikin wani bincike cewa Bankin DBN a cikin shekarar 2021, ta rabar da kudi kusan kimanin rabin Tiriliyan, amma abun takaici shi ne inda talauci ya fi katutu kuma inda ake bukatar a farfado da kananan masana’antu ba su samu ko rabin abin da suka rabar ba.

“Na gano cewa Jihar Legas kadai a cikin Kudi naira Biliyan 483 sun samu kashi 47% amma sauran shiyyar Kudu maso yamma sun samu kashi 10 wanda gaba daya kudin ya kama naira Tiriliyan 274 a yayin da daga cikin Jihohi shida na Kudu maso yamma, ita Jihar Legas kadai ke da Kudi kimanin naira Biliyan 227 amma sauran Jihohin biyar ke da kashi 10.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

“Haka Kudu maso Kudu sun samu kashi 17 da ya kama Naira Biliyan 81, amma gaba dayan Arewa da ke da Jahohi 19 sun samu kashi 11 wanda ya kama kimanin naira Biliyan 53, domin a shiyyar Arewa maso gabas ta samu kashi 5 wato naira Biliyan 24, sai shiyyar Arewa maso yamma ta samu kashi daya wato Naira Biliyan 4,820.

 

“Makasudin kafa wannan Bankin shi ne don ta taimaka wa kananan `yan Kasuwa da masana’antu wanda sune ke fannin Noma, kasuwanci, sufuri amma sai muka ga sun dauki kashi 42 na kudin sun ba masu harkar mai.

 

“Kudin da aka bayar ga shiyyoyin 6 bashi ne ake bayarwa mai sassauci don farfado da tattalin Arzikin Kasa ta hanyar Bankin don ita Bankin da za ta bayar, ba tana bayarwa ba ne don riba sai don a taimaka.

“Misali a Jihar Kano da Sokoto an rufe masana’antu da yawa don ba Kudin da za a farfado da su, shi ne ya sa ake so a basu wannan kudin da zai zamanto ba za a kuntata musu ba, toh amma kwalliya ba ta biya kuɗin sabulu ba.

Acewarsa, akwai bukatar a yi bincike don sanin shin nawa ne Kudin, mai yasa aka rabar da kudin haka, meye za ayi don tabbatar cewa dalilin da ya sa aka kafa wannan Banki da kuma tabbatar da cewa Kudaden da ake rabar sun je ga hannun wadanda ya kamata, kuma `yan Nijeriya su gani a kasa ta hanyar tabbatar da cewa kananan masana’antu na tasowa ta hanyar taimakon wannan Banki tunda a bisa wannan dalilin ya sa aka kafa Bankin na DBN.

“Kuma akwai Bankin Kasuwanci (BOI), NIRSAL ta CBN da Gwamnatin Tarayya da suka sha fitar da wadansu hanyoyin da tsari don taimaka wa `yan Nijeriya talakawa amma har yanzu ba a gani a Kasa ba saboda matsalar wadanda aka saka su su yi aikin ya sa muke son mu yi bincike a Majalisar domin idan da akwai wadanda suka hana ruwa gudu, sai a san yadda za a yi a kawar da su domin a samu tsari mai kyau a kan abin da ake bukata.

“An hada kwamitin wucin Gadi na mutum bakwai, an saka ni member kuma Inshaa Allah za mu tabbatar da cewa an yi abun da ya dace don tabbatar da cewa `yan Nijeriya sun ga abin da aka yi tare da tabbatar cewa an yi maganin matsalar.

“A yanzu talauci ya addabi `yan Nijeriya musamman Arewa. A kiyasi, Jihar Kebbi na fama da talauci kimanin kashi 86, Jihar Gombe 77, Jihar Bauchi 87, Jihar Taraba 78, Jihar Zamfara kashi 80, sannan kusan rabin Jihar Filato na fama da talauci, haka sama da rabin `yan Jihar Ebonyi su ma suna fama da talauci, shi yasa ni a matsayin wakili na kai wannan lamarin gaban Majalisar don a yi wa tubkar hanci, a yi maganin lamarin kuma `yan uwana `yan majalisar sun karbi abun hannu biyu-biyu, don haka suka bani goyon baya.” Inji Ndume


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Ganawa Tsakanin Ministocin Tsaron Kasashen Sin Da Amurka 

Next Post

Matafiya 17 Da Suka Taso Daga Legas Zuwa Gombe Sun Kone Kurmus A Hadarin Mota

Related

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

43 minutes ago
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu
Labarai

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

3 hours ago
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 
Labarai

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

7 hours ago
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
Labarai

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

9 hours ago
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo
Labarai

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

9 hours ago
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa
Labarai

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

10 hours ago
Next Post
Matafiya 17 Da Suka Taso Daga Legas Zuwa Gombe Sun Kone Kurmus A Hadarin Mota

Matafiya 17 Da Suka Taso Daga Legas Zuwa Gombe Sun Kone Kurmus A Hadarin Mota

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.