• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Bukaci Manyan Masu Kalubalantarsa Atiku Da Obi Da Su Janye Daga Takara

Ya Samu Sarautar Gargajiya A Delta

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Manyan Labarai, Siyasa
0
Zan Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa Kamar Yadda Buhari Ya Yi – Tinubu 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar shugabancin kasar na jam’iyyar APC a zaben 2023, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya shawarci manyan abokan karawarsa, Atiku Abubakar da Peter Obi da su hakura su bar masa neman shugabancin kasar nan.

Tinubu, wanda ya bayyana hakan a ranar Juma’a a  masarautar garin Gbaramatu da ke karamar hukumar Warri a kudu Maso Yamma, ya ce, Atiku wanda shi ne dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, ya jima lokuta da dama yana neman kujerar ba tare da ya samu nasara ba, don haka da bukatar ya janye muradinsa na sake neman a 2023.

  • Zamanintar Da Sha’anin Gona Da Kauyuka Ya Dogaro Da Halin Da Ake Ciki Da Muradun Jama’a
  • Ko Kun San Gida Mafi Tsada A Duniya?

Da ya ke magana da Pere na Gbaramatu, Oboro-Gbaraun II, Aketekpe, Agadagba da kuma dandazon magoya bayansa a masarautar Basaraken, Tinubu ya ce: “Sau nawa Atiku na neman mulkin nan? Ko da yake Atiku na kan nema, ku fada masa ya koma gefe kawai ya zauna, hakan ya isa.”

Kan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour (LP), Peter Obi, Asiwaju Bola ya ce, lissafin kididdigar Obi da nazarinsa kan tattakin arziki dukkaninsu cike suke da tukin kuskure.

“Ba na son jero sunaye, yana tunanin kididdigar da zai bai wa ‘yan Nijeriya abinci ne? Ya na bada kididdiga marar kyau, tattakin arziki marar kyau. Ba wannan al’ummar Nijeriya ke bukata ba,” Tinubu ya fada wa Obi.

Labarai Masu Nasaba

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Tinubu, wanda aka nada masa Sarautar Iyelawei na masarautar Gbaramatu Kingdom da Sarkin ya ba shi, ya sha alwashin cika dukkanin alkawuran da ya yi, ya kuma yi alkawarin samar da abubuwan cigaba ga al’ummar Gbaramatu, musamman a bangaren shimfida titina, Jami’a, da sauransu, ya ce ba zai taba yin nisa da masarautar ba.

“Zan ci gaba da neman shawarorin Sarki domin cigaban masarautar Gbaramatu, don yin aiki wajen bunkasa tattalin arziki”.

Wadanda suka yi wa Tinubu rakiya sun hada da gwamnonin Kano, Abdulahi Ganduje, Mai Mala Buni na Yobe; karamin ministan albarkatun Mai, Timipre Silva; karamin ministan kwadago, Festus Keyamo; Dimeji Bankole, da tsohon ministan kula da harkokin Niger Delta Affairs, Elder Godsday Orubebe, da sauransu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 2023APCAtikuLPPDPtakaraTinubuZaben Shugaban Kasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ko Kun San Gida Mafi Tsada A Duniya?

Next Post

Gwamnatin Kaduna Ta Jajanta Wa Iyalan Mutane 15 Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe

Related

An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

16 minutes ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

2 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

3 hours ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

4 hours ago
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

9 hours ago
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta
Siyasa

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

19 hours ago
Next Post
Gwamnatin Kaduna Ta Jajanta Wa Iyalan Mutane 15 Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe

Gwamnatin Kaduna Ta Jajanta Wa Iyalan Mutane 15 Da 'Yan Bindiga Suka Kashe

LABARAI MASU NASABA

An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

June 28, 2025
Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

June 28, 2025
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

June 28, 2025
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.