ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Bukaci Manyan Masu Kalubalantarsa Atiku Da Obi Da Su Janye Daga Takara

Ya Samu Sarautar Gargajiya A Delta

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Tinubu

Dan takarar shugabancin kasar na jam’iyyar APC a zaben 2023, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya shawarci manyan abokan karawarsa, Atiku Abubakar da Peter Obi da su hakura su bar masa neman shugabancin kasar nan.

Tinubu, wanda ya bayyana hakan a ranar Juma’a a  masarautar garin Gbaramatu da ke karamar hukumar Warri a kudu Maso Yamma, ya ce, Atiku wanda shi ne dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, ya jima lokuta da dama yana neman kujerar ba tare da ya samu nasara ba, don haka da bukatar ya janye muradinsa na sake neman a 2023.

  • Zamanintar Da Sha’anin Gona Da Kauyuka Ya Dogaro Da Halin Da Ake Ciki Da Muradun Jama’a
  • Ko Kun San Gida Mafi Tsada A Duniya?

Da ya ke magana da Pere na Gbaramatu, Oboro-Gbaraun II, Aketekpe, Agadagba da kuma dandazon magoya bayansa a masarautar Basaraken, Tinubu ya ce: “Sau nawa Atiku na neman mulkin nan? Ko da yake Atiku na kan nema, ku fada masa ya koma gefe kawai ya zauna, hakan ya isa.”

ADVERTISEMENT

Kan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour (LP), Peter Obi, Asiwaju Bola ya ce, lissafin kididdigar Obi da nazarinsa kan tattakin arziki dukkaninsu cike suke da tukin kuskure.

“Ba na son jero sunaye, yana tunanin kididdigar da zai bai wa ‘yan Nijeriya abinci ne? Ya na bada kididdiga marar kyau, tattakin arziki marar kyau. Ba wannan al’ummar Nijeriya ke bukata ba,” Tinubu ya fada wa Obi.

LABARAI MASU NASABA

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

Tinubu, wanda aka nada masa Sarautar Iyelawei na masarautar Gbaramatu Kingdom da Sarkin ya ba shi, ya sha alwashin cika dukkanin alkawuran da ya yi, ya kuma yi alkawarin samar da abubuwan cigaba ga al’ummar Gbaramatu, musamman a bangaren shimfida titina, Jami’a, da sauransu, ya ce ba zai taba yin nisa da masarautar ba.

“Zan ci gaba da neman shawarorin Sarki domin cigaban masarautar Gbaramatu, don yin aiki wajen bunkasa tattalin arziki”.

Wadanda suka yi wa Tinubu rakiya sun hada da gwamnonin Kano, Abdulahi Ganduje, Mai Mala Buni na Yobe; karamin ministan albarkatun Mai, Timipre Silva; karamin ministan kwadago, Festus Keyamo; Dimeji Bankole, da tsohon ministan kula da harkokin Niger Delta Affairs, Elder Godsday Orubebe, da sauransu.

Tinubu
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

MASU ALAKA

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai
Manyan Labarai

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

June 14, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki
Labarai

Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

June 14, 2026
Sowore Ya Yi Kira Ga Zanga-Zangar Kasa Kan Tinubu Ranar Litinin
Manyan Labarai

Sowore Ya Yi Kira Ga Zanga-Zangar Kasa Kan Tinubu Ranar Litinin

June 14, 2026
Next Post
Gwamnatin Kaduna Ta Jajanta Wa Iyalan Mutane 15 Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe

Gwamnatin Kaduna Ta Jajanta Wa Iyalan Mutane 15 Da 'Yan Bindiga Suka Kashe

LABARAI MASU NASABA

An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

June 15, 2026
An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

June 15, 2026
Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

June 15, 2026
Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

June 14, 2026
Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

June 14, 2026
Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

June 14, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

June 14, 2026
An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 14, 2026
Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

June 14, 2026
Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

June 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.