• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’an DSS Sun Cafke Wani Babban Kwamandan ISWAP A Kano

by Muhammad
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Jami’an DSS Sun Cafke Wani Babban Kwamandan ISWAP A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar tsaron farin kaya ta DSS a Nijeriya ta tabbatar da cafke wani da take zargin ɗaya ne daga cikin manyan kwamandojin kungiyar ‘Yan ta’adda ta ISWAP ne a Kano.

BBC ta rawaito cewa, Rundunar tsaron ta dai kama wanda ake zargin tare da wasu daga cikin yaransa a daidai lokacin da suke shirya kai wasu hare-hare na ta’addanci a Kano.

  • Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor
  • An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai

Mutumin, wanda jami’an DSS suka kama da ake yi wa laƙabi da Malam Abba, an kama shi ne a unguwar Samegu a yankin karamar hukumar Kumbotso a Kano.

DSS ta ce ta sami nasarar kama Malam Abba da waɗanda aka kama shi da su bayan samun wasu bayanan sirri.

Sannan wanda ake zargin shi ne mai bayar da horo, da shirya hare-haren da ISWAP din za ta kai a jihar.

Labarai Masu Nasaba

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

Wannan dai na zuwa ne a dai-dai lokacin da babban hafsan tsaro Nijeriya janar Lucky Irabor ke cewa rudunar tsaron kasar ta daƙile wani yunƙurin kai hari a Kano wanda suka ce zai iya zama “mafi muni” a ƙasar.

Janar Irabor ya ƙara da cewar sun daƙile harin ne a Kano cikin makon da aka kai hari wata coci da ke garin Owo na Jihar Ondo, wanda ‘yan bindiga suka kashe fiye da mutum 40.

Sannan sun gano kayayyakin da ake haɗa abubuwan fashewa da su, tare da ƙwace ƙunshin makamai masu yawan gaske da miyagu ke ƙoƙarin yin amfani da su a sassan ƙasar ciki har da Abuja.

Idan za a iya tunawa a ranar 17 ga watan Mayu aka sami fashewar wata tukunyar gas a titin Aba da ke Sabon gari a Kano, da ya yi sanadiyar mutuwar mutum tara tare da jikkata wasu da dama.

Sai dai an sami rabuwar kai tsakanin al’umma mazauna yankin da jami’an tsaro, inda mazauna yankin ke cewa bom ne, yayin da jami’an tsaro ke cewar tukunyar gas ce da ke waje ta fashe.

Haka zalika kwanaki kadan da faruwar wannan al’amari rudunar ƴan sandan Kano ta ce ta ga wata mota maƙare da kayan hada bom a unguwar Bugaje a yankin karamar hukumar Kumbotso.

Jami’an tsaron sun yi zargin cewar an shiga da motar ne daga jihar Jigawa da ke maƙwabtaka da Kanon.

Tuni dai hukumomi a Nijeirya suka tabbatar da ayyukan Mayakan ISWAP a jihar Kaduna da wasu dazuzzuka da ke arewa maso yammacin Nijeirya, da ake fama da matsalolin masu garkuwa da mutane.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Lawan Na Fuskantar Barazanar Rasa Kujerarsa Wanda Ya Maye Gurbinsa Ya Ki Janye Masa

Next Post

Kungiyar ‘Yan Ta’adda Ta Ansaru Ta Ce Ba Ita Ta Kai Hari Kan Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Ba

Related

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

4 hours ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

6 hours ago
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

9 hours ago
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
Manyan Labarai

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

13 hours ago
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
Manyan Labarai

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

14 hours ago
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

1 day ago
Next Post
Kungiyar ‘Yan Ta’adda Ta Ansaru Ta Ce Ba Ita Ta Kai Hari Kan Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Ba

Kungiyar 'Yan Ta'adda Ta Ansaru Ta Ce Ba Ita Ta Kai Hari Kan Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Ba

LABARAI MASU NASABA

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

September 17, 2025
Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

September 17, 2025
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.