ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar ‘Yan Ta’adda Ta Ansaru Ta Ce Ba Ita Ta Kai Hari Kan Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Ba

by Muhammad
4 years ago
Kungiyar

Ƙungiyar ‘Yan ta’adda ta Ansaru mai alaƙa da Kungiyar Al-Qaeda da ke ayyukanta a arewa maso yammacin Najeriya ta yi watsi da zargin da ake mata na hannu a harin da aka kai kan jirgin ƙasan Abuja zuwa Kaduna ranar 28 ga watan Maris din 2022.

Kafar yada labari ta BBC ta rawaito cewa, a ƙalla mutum tara ne suka mutu a harin, sannan an sace wasu, wasu kuma suka ɓata.

  • Jami’an DSS Sun Cafke Wani Babban Kwamandan ISWAP A Kano
  • Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor

Ansaru ta ƙaryata zargin ne a wani saƙo na bidiyo da ta saki ranar 12 ga watan Yuni a shafukanta na Telegram da RocketChat.

ADVERTISEMENT

Mai magana a cikin bidiyon ya yi jawabin ne da Larabci sannan ya yi da Hausa.

An ga a ƙalla mutum bakwai a bidiyon dukkansu sanye da takunkumin rufe fuska kuma suna ɗauke da bindigogi.

LABARAI MASU NASABA

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Mutumin da ke bayanin wanda ba a iya gane shi, ya tsaya a tsakiya ne yana magana kan abin da ya kira “labarin ƙarya da yake yaɗuwa cewa ƙungiyar Ansarul al-Muslimin fi bilad al-Sudan (cikakken sunan ƙungiyar) ta ɗauki alhakin kai harin jirgin ƙasan.”

Ya ƙara da cewa “wannan ƙarya ce tsagwaronta wacce ba ta da tushe.”

Ya ce Ansaru ba ta da hannu ko kaɗan a harin jirgin ko sace fasinjojinsa.

Hukumomi a Nijeriya sun zargi Ansaru, wacce ke ayyukanta a yankin, da kuma ƙungiyar Boko Haram, wacce take da ƙarfi a arewa maso gabas, da hannu a kai wa jirgin ƙasan hari, ko dai kai tsaye ko kuma ta hanyar hada kai da ƴan bindigar da suke ayyukansu a yankin.

Ƴan bindigar sun yi ta sakin bidiyo da hotuna na mutanen da aka kama a jirgin tun bayan harin.

Mai magana a madadin Ansaru din ya ce an tsara “labarin ƙaryar” ne don a zubar wa ƙungiyar mutunci, inda ya jaddada cewa tana ƙoƙarin kaucewa cin zarafin ƴan yankin kuma tana taɓa waɗanda suke adawa ko fito na fito da ita ne kawai.

Tun bayan da ta fara ayyukanta a yankin arewa maso yammacin Nijeriya a farko-farkon shekarar 2021, a lokacin da ta bayyana mubaya’arta ga ƙungiyar al-Qaeda, Ansaru ta matsa wajen nesanta kanta da amfani da tsauraran hanyoyin masu ikirarin jihadi kamar su Boko Haram da IS da kuma ayyukan ƴan binciga.

A wani saƙonta na baya-baya, Ansaru ta nanata cewa tana neman hadin kan mutane ne ta hanyar da’awa maimakon yaƙarsu.

Mai maganar ya ce Ansaru ta yi amannar cewa harin jirgin ƙasan ba shi da alaƙa da jihadi kuma yin hakan ma jawo fitina ne kuma ya saɓa wa Musulunci da aƙidar masu jihadi.

Kungiyar
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036
Labarai

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina
Labarai

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Next Post
Mai Yiwuwa Ne Matakan Sin Na Iya Maida Komadar Tattalin Arzikin Duniya

Mai Yiwuwa Ne Matakan Sin Na Iya Maida Komadar Tattalin Arzikin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

July 4, 2026
Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

July 4, 2026
Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.