• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP Ta Fito Da Sabon Salon Yakin Neman Zabe A Sakkwato

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
3 years ago
in Siyasa
0
PDP Ta Fito Da Sabon Salon Yakin Neman Zabe A Sakkwato
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babba jigo a kwamitin yakin neman zaben Jam’iyyar PDP a Jihar Sakkwato, Honarabul Aminu Bala Bodinga ya bayyana cewar jam’iyyar a Jihar ta fito da sabon salon yakin neman zabe ne domin kawar da matsaloli da kalubalen da jam’iyyar ke fuskanta domin samun nasarar Babban Zaben 2023.

  • An Tsige Shugaban Jam’iyyar NNPP A Kaduna

Honarabul Aminu Bala wanda kuma shine Kwamishinan Filaye da Gidaje ya bayyana cewar sabon salon yakin neman zabe da suka bullo da shi mai tasiri ne da alfanu ga jam’iyyar PDP da al’ummar Jihar Sakkwato bakidaya.

Jigon dan siyasar ya bayyana hakan ne a yau a tattaunawarsa da manema labarai a wajen ci- gaba da taron masu ruwa da tsaki da jam’iyyar PDP ke gudanarwa da Karamar Hukumar Gudu a otel din Giginya.

Ya ce sabon salo ne suka fito da shi domin zama da kowace Karamar Hukuma a tattauna ido da ido a baje siyasa da matsalolinta a faifai akasin yadda ake yi a can baya. Ya ce a yanzu su kan zauna da dukkanin masu ruwa da tsaki a lamurran jam’iyya, a saurari matsaloli ta yadda wadanda ake iya gyarawa a gyara kai tsaye wadanda kuma ake alkawali sai a dauki alkawali zuwa bayan zabe.

Ya ce wani muhimmin lamari shine ko da akwai ‘ya’yan jam’iyya wadanda ke da sabani da juna, ba za a kammala taron ba sai an daidata su an fahimci juna, don haka ya bayyana cewar muhimmancin taron ya fi gaban a nanata.

Labarai Masu Nasaba

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

ÆŠaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

“Tarukan da ake zuwa yakin neman zabe a Kananan Hukumomi shugabanni ne kawai ke samun damar magana ba tare da bayar da dama ga dukkanin jama’a su samu damar cewa wani abu ba, ko gabatar da korafi ba saboda rashin lokaci amma a wannan taron na masu ruwa da tsaki, akwai cikakken lokaci da damar sauraren kowa da kowa.” Ya bayyana.

“Misali a yanzu Karamar Hukumar Gudu ce muke zama da ita, kuma zaben 2019 da ya gabata mun samu gagarumar nasara a Gudu 100%, don haka a wannan zaben ma akalla muna son ka da mu kasa samun kashi 90% in sha Allah.”

A taron wanda Shugaban Kwamitin Yakin Neman Zaben PDP a Jihar, Tsohon Ministan Sufuri, Honarabul Yusuf Sulaiman ya jagoranta ya bayyana za su aiwatar da kakkarfan kamfen din da zai tabbatar da samun nasarar jam’iyyar PDP a dukkanin matakai daga sama har kasa bakidaya.

A jawabinsa Mataimakin Dan Takarar Gwamnan Jihar Sakkwato, Honarabul Sagir Bafarawa ya bayyana cewar Karamar Hukumar Gudu ta jam’iyyar PDP ce gaba da baya don haka ba su da shakku a kan ta.

“Gudu ko kadan ba wajen zuwan APC ba ne, al’ummar Gudu bakidaya PDP suke yi domin ita ce jam’iyyar da suka yi amannar za ta rika kawar da matsalolin su da inganta jin dadin su.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Tsige Shugaban Jam’iyyar NNPP A Kaduna

Next Post

‘Yan Daba Sun Raunata Soja Da ‘Yan Kwana-Kwana 2 Yayin Da Gobara Ta Tashi A Gidan Mai A Kwara

Related

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro
Manyan Labarai

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

8 hours ago
ÆŠaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci
Siyasa

ÆŠaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

1 day ago
Labarai

ÆŠaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

3 days ago
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC
Labarai

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

3 days ago
Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 
Siyasa

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

5 days ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

6 days ago
Next Post
‘Yan Daba Sun Raunata Soja Da ‘Yan Kwana-Kwana 2 Yayin Da Gobara Ta Tashi A Gidan Mai A Kwara

'Yan Daba Sun Raunata Soja Da ‘Yan Kwana-Kwana 2 Yayin Da Gobara Ta Tashi A Gidan Mai A Kwara

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

August 27, 2025
Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

August 27, 2025
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.