ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP Ta Fito Da Sabon Salon Yakin Neman Zabe A Sakkwato

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
4 years ago
PDP

Babba jigo a kwamitin yakin neman zaben Jam’iyyar PDP a Jihar Sakkwato, Honarabul Aminu Bala Bodinga ya bayyana cewar jam’iyyar a Jihar ta fito da sabon salon yakin neman zabe ne domin kawar da matsaloli da kalubalen da jam’iyyar ke fuskanta domin samun nasarar Babban Zaben 2023.

  • An Tsige Shugaban Jam’iyyar NNPP A Kaduna

Honarabul Aminu Bala wanda kuma shine Kwamishinan Filaye da Gidaje ya bayyana cewar sabon salon yakin neman zabe da suka bullo da shi mai tasiri ne da alfanu ga jam’iyyar PDP da al’ummar Jihar Sakkwato bakidaya.

Jigon dan siyasar ya bayyana hakan ne a yau a tattaunawarsa da manema labarai a wajen ci- gaba da taron masu ruwa da tsaki da jam’iyyar PDP ke gudanarwa da Karamar Hukumar Gudu a otel din Giginya.

ADVERTISEMENT

Ya ce sabon salo ne suka fito da shi domin zama da kowace Karamar Hukuma a tattauna ido da ido a baje siyasa da matsalolinta a faifai akasin yadda ake yi a can baya. Ya ce a yanzu su kan zauna da dukkanin masu ruwa da tsaki a lamurran jam’iyya, a saurari matsaloli ta yadda wadanda ake iya gyarawa a gyara kai tsaye wadanda kuma ake alkawali sai a dauki alkawali zuwa bayan zabe.

Ya ce wani muhimmin lamari shine ko da akwai ‘ya’yan jam’iyya wadanda ke da sabani da juna, ba za a kammala taron ba sai an daidata su an fahimci juna, don haka ya bayyana cewar muhimmancin taron ya fi gaban a nanata.

LABARAI MASU NASABA

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

“Tarukan da ake zuwa yakin neman zabe a Kananan Hukumomi shugabanni ne kawai ke samun damar magana ba tare da bayar da dama ga dukkanin jama’a su samu damar cewa wani abu ba, ko gabatar da korafi ba saboda rashin lokaci amma a wannan taron na masu ruwa da tsaki, akwai cikakken lokaci da damar sauraren kowa da kowa.” Ya bayyana.

“Misali a yanzu Karamar Hukumar Gudu ce muke zama da ita, kuma zaben 2019 da ya gabata mun samu gagarumar nasara a Gudu 100%, don haka a wannan zaben ma akalla muna son ka da mu kasa samun kashi 90% in sha Allah.”

A taron wanda Shugaban Kwamitin Yakin Neman Zaben PDP a Jihar, Tsohon Ministan Sufuri, Honarabul Yusuf Sulaiman ya jagoranta ya bayyana za su aiwatar da kakkarfan kamfen din da zai tabbatar da samun nasarar jam’iyyar PDP a dukkanin matakai daga sama har kasa bakidaya.

A jawabinsa Mataimakin Dan Takarar Gwamnan Jihar Sakkwato, Honarabul Sagir Bafarawa ya bayyana cewar Karamar Hukumar Gudu ta jam’iyyar PDP ce gaba da baya don haka ba su da shakku a kan ta.

“Gudu ko kadan ba wajen zuwan APC ba ne, al’ummar Gudu bakidaya PDP suke yi domin ita ce jam’iyyar da suka yi amannar za ta rika kawar da matsalolin su da inganta jin dadin su.”

PDP
Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
+ postsBio
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Taƙaddamar Kafa Hukumar Bogi: Tinubu Ya Umarci A Yi Binciken Ƙwaƙwaf
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Shekara 200 Bayan Shehu Ɗan Fodiyo: Hubbarensa Na Ci Gaba Zama Wajen Ziyara Da Neman Tabarruki
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
Siyasa

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Next Post
‘Yan Daba Sun Raunata Soja Da ‘Yan Kwana-Kwana 2 Yayin Da Gobara Ta Tashi A Gidan Mai A Kwara

'Yan Daba Sun Raunata Soja Da ‘Yan Kwana-Kwana 2 Yayin Da Gobara Ta Tashi A Gidan Mai A Kwara

LABARAI MASU NASABA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.