ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP Ta Fito Da Sabon Salon Yakin Neman Zabe A Sakkwato

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
4 years ago
PDP

Babba jigo a kwamitin yakin neman zaben Jam’iyyar PDP a Jihar Sakkwato, Honarabul Aminu Bala Bodinga ya bayyana cewar jam’iyyar a Jihar ta fito da sabon salon yakin neman zabe ne domin kawar da matsaloli da kalubalen da jam’iyyar ke fuskanta domin samun nasarar Babban Zaben 2023.

  • An Tsige Shugaban Jam’iyyar NNPP A Kaduna

Honarabul Aminu Bala wanda kuma shine Kwamishinan Filaye da Gidaje ya bayyana cewar sabon salon yakin neman zabe da suka bullo da shi mai tasiri ne da alfanu ga jam’iyyar PDP da al’ummar Jihar Sakkwato bakidaya.

Jigon dan siyasar ya bayyana hakan ne a yau a tattaunawarsa da manema labarai a wajen ci- gaba da taron masu ruwa da tsaki da jam’iyyar PDP ke gudanarwa da Karamar Hukumar Gudu a otel din Giginya.

ADVERTISEMENT

Ya ce sabon salo ne suka fito da shi domin zama da kowace Karamar Hukuma a tattauna ido da ido a baje siyasa da matsalolinta a faifai akasin yadda ake yi a can baya. Ya ce a yanzu su kan zauna da dukkanin masu ruwa da tsaki a lamurran jam’iyya, a saurari matsaloli ta yadda wadanda ake iya gyarawa a gyara kai tsaye wadanda kuma ake alkawali sai a dauki alkawali zuwa bayan zabe.

Ya ce wani muhimmin lamari shine ko da akwai ‘ya’yan jam’iyya wadanda ke da sabani da juna, ba za a kammala taron ba sai an daidata su an fahimci juna, don haka ya bayyana cewar muhimmancin taron ya fi gaban a nanata.

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

“Tarukan da ake zuwa yakin neman zabe a Kananan Hukumomi shugabanni ne kawai ke samun damar magana ba tare da bayar da dama ga dukkanin jama’a su samu damar cewa wani abu ba, ko gabatar da korafi ba saboda rashin lokaci amma a wannan taron na masu ruwa da tsaki, akwai cikakken lokaci da damar sauraren kowa da kowa.” Ya bayyana.

“Misali a yanzu Karamar Hukumar Gudu ce muke zama da ita, kuma zaben 2019 da ya gabata mun samu gagarumar nasara a Gudu 100%, don haka a wannan zaben ma akalla muna son ka da mu kasa samun kashi 90% in sha Allah.”

A taron wanda Shugaban Kwamitin Yakin Neman Zaben PDP a Jihar, Tsohon Ministan Sufuri, Honarabul Yusuf Sulaiman ya jagoranta ya bayyana za su aiwatar da kakkarfan kamfen din da zai tabbatar da samun nasarar jam’iyyar PDP a dukkanin matakai daga sama har kasa bakidaya.

A jawabinsa Mataimakin Dan Takarar Gwamnan Jihar Sakkwato, Honarabul Sagir Bafarawa ya bayyana cewar Karamar Hukumar Gudu ta jam’iyyar PDP ce gaba da baya don haka ba su da shakku a kan ta.

“Gudu ko kadan ba wajen zuwan APC ba ne, al’ummar Gudu bakidaya PDP suke yi domin ita ce jam’iyyar da suka yi amannar za ta rika kawar da matsalolin su da inganta jin dadin su.”

PDP
Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
+ postsBio
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Zulum Ya Ƙaddamar Da Gidajen Ƴan Gudun Hijira 100 A Sakkwato
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Siyasar 2027: Yadda Ƴan Adawa Ke Ƙara Shiga Tsaka-mai-wuya

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
‘Yan Daba Sun Raunata Soja Da ‘Yan Kwana-Kwana 2 Yayin Da Gobara Ta Tashi A Gidan Mai A Kwara

'Yan Daba Sun Raunata Soja Da ‘Yan Kwana-Kwana 2 Yayin Da Gobara Ta Tashi A Gidan Mai A Kwara

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.