ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Daba Sun Raunata Soja Da ‘Yan Kwana-Kwana 2 Yayin Da Gobara Ta Tashi A Gidan Mai A Kwara

by Sadiq
4 years ago
Kwara

Wasu ‘yan daba sun kai wa wani soja da jami’an kashe gobara biyu na Jihar Kwara hari tare da raunata su yayin da suke aikin ceto a wani gidan mai da gobara ta kone a Ilorin, babban birnin jihar.

An kai sojan da jami’an hukumar kashe gobara ta jihar zuwa gidan man K&R da ke unguwar Oke Agodi a cikin birnin Ilorin, domin kashe wutar da ta tashi da misalin karfe 9:30 na dare.

  • Hisbah Ta Kama Motoci 3 Makare Da Giya A Kano
  • An Cafke Wasu Ma’aurata Kan Zargin Hada Baki Wajen Bizne Jaririyarsu Da Ranta A Jigawa

Amma, ‘yan daban suka fara jifan sojoji da jami’an kashe gobara inda ana haka suka jikkata soja daya da ‘yan kwana-kwana biyu.

ADVERTISEMENT

LEADERSHIP ta tattaro cewa daga karshe sojojin sun dawo da zaman lafiya a yankin yayin da ‘yan kwana-kwana suka samu nasarar kashe gobarar.

Sai dai gobarar ta cinye motoci biyu da ofisoshi biyu kafin ‘yan kwana-kwana su kashe ta.

LABARAI MASU NASABA

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Kimanin kadarar Naira 21.7m aka yi asara a gobarar yayin da kiyasin dukiyar da aka ceto daga gobarar ta kai Naira 48.4million.

Kakakin hukumar kashe gobara ta Jihar Kwara, Hassan Adekunle, a wata sanarwa a ranar Laraba, ya tabbatar da barkewar gobarar da harin da aka kai kan sojoji da ‘yan kwana-kwana.

Sanarwar ta kara da cewa: “A jiya Talata 6 ga Disamba, 2022, wasu ‘yan daba a Unguwar Oke-Agodi Alfa Yahaya da ke Ilorin sun kai hari kan jami’an hukumar kashe gobara ta Jihar Kwara tare da raunata wasu jami’an kashe gobara guda biyu a gidan man K&R Petroleum Nigeria Limited.

“Daya daga cikin tawagar sojojin Nijeriya da suka zo kwantar da tarzoma su ma sun yi ta harbin kan mai uwa da wabi, hasali ma dai wannan sojan ya samu rauni.

“Saboda haka, daraktan hukumar kashe gobara ta Jihar Kwara, Prince Falade John Olumuyiwa, ya bayyana alhininsa game da faruwar lamarin tare da bayyana al’ummar yankin Agodi a matsayin masu nuna rashin godiya da rashin yaba wa kokarin ‘yan kwana-kwana.”

MASU ALAKA

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe
Manyan Labarai

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Next Post
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Isa Birnin Riyadh Kasar Saudiyya

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Isa Birnin Riyadh Kasar Saudiyya

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026
Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.