• English
  • Business News
Friday, August 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Kara Tsaurara Tsaro A Hanyoyinmu

by Bello Hamza
3 years ago
in Rahotonni
0
A Kara Tsaurara Tsaro A Hanyoyinmu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A watan Janairu na wannan shekarar aka samu rahoton garkuwa da mutane a kan babbar hanyar Legas zuwa Ibadan. Hanyar ta kasance hanyar data fi daukar zirga-zirgar motoci a kasar nan, tana daukar mutane da kayyaki daga Arewaci zuwa Kudancin kasar nan.

A wani hari da ‘yan bindiga suka kai kwanan nan a daidai kauyen Abule Onigari inda suka kashe wani Direban motar haya, suka kuma yi awon gaba da fasinjoji 5. Kwana daya bayan nan kuma a daidai wurin da aka yina baya sai gashi ‘yan bindigan sun sake kai hari inda suka sace wata fittaciyar ‘yar fim mai suna, Bimpe Akintunde da ‘yarta. Tun daga wannan lokacin kuma sai rahottanin garkuwa da mutane a kan wannan babbar hanyar da ke da magtukar muhimmanci a zirga-zirgar mutane da kayyaki a tsakanin Arewaci da Kudancin Nijeriya ya cigaba da karuwa.

  • Gwamnatin Ebonyi Ta Ba Da Umarnin Kashe Duk Wanda Aka Gani Da Bindiga 

Matafiya da dama ciki har da Tsohon Mataimakin Shugaban Jami’ar Ibadan Farfesa Adigun Agbaje da wasu dalibai sun shiga hannun masu garkuwa da mutane a ranar 28 ga watan Oktoba, an sako ne bayan da aka biya wasu makudan kudade. Bayani ya nuna cewa, yawancin masu garkuwa da mutane na shigar sojoji ne yayin gudanar da ayyukansu.

Rahoton ‘yansanda ya nuna cewa, an kai harin ne a kusa da Jami’ar Dominion da ke a bangare na karshen babbar hanyar Legas zuwa Ibadan, ‘yansanda sun bayyana yadda suka kai daukin gaggawa a karkashin jagorancin babban jami’in ‘yansanda na yankin, DPO da ‘yansanda Mobayil da gungun mafarauta suka kai daukin ceto mutanen a inda daya daga cikin ‘yansandan ya rasa ransa wasu kuma suka ji munanan raunuka, suna asibiti a halin yanzu suna karbar magani.

Yawaitar faruwar wannan ya fara zama wani kalubale ga mahukunta a halin yanzu. Haka kuma bayani ya nuna cewa, ‘yanbindigar na sanye ne da cikakkun kayan sojoji a yayin da suka datse hanyar. Abin lura a nan shi ne ayyukan wadannan ‘yan ta’addar ba su bar kowa ba a kan hanyoyin namu. In har wannan hare-haren suka ci gaba za su haifar da asarar rayuka da dukiyoyin al’umma masu dinbin yawa.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Amma ba wai a kan hanyoyinmu ne kadai ake fuskantar wannan barazanar ba. Kwanakin baya a cikin watan Yuni, an yi garkuwa da jami’a 10 na rundunar ‘yansandan Jihar Nasarawa a kan hanyarsu ta dawowa daga aikin sa ido a zaben gwamnan jihar Osun har zuwa wannan lokacin babu wani duriyar su. Bayani ya nuna cewa, an sace ‘yansandan ne a garin Obajana na Jihar Kogi a ranar 17 ga watan Yuli 2022, a daidai wurin da tireloli ke farkin da ake kira da ‘PTI Obajana’.

A daidai wannan lokacin na shekara da zirga-zirgar abin hawa ke kara karuwa, lokacin ne kuma da harkokin ‘yan ta’adda ke kaiwa makura. Kuma abubuwan kenan da ke faruwa a manyan hanyoyinmu a fadin tarayyar kasar nan.

Tuni ‘yan Nijeriya suka fara mantawa da kirga yawan garkuwa da mutanen da ake yi a kan babbar hanyar Abuja zuwa Kaduna dama hanyar Birnin Gwari zuwa Kaduna. Kasar bata kai ga farfadowa daga garkuwan da aka yi wa fasinjojin jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna ba, inda wadanda aka yi garkuwa da su suka yi fiye da watannin 8 a hannun ‘yan bindiga.

Ana zargin an biya ‘yan bindigan Billiyoyin Naira a mastayin kudin fansa kafin a kai ga sako kashi na karshe na mutanen kwanan nan. A yau babu wani magana a kan gudanar da cikakken bincike ballatana a kai ga hukunta wadanda suka aikata wannan laifin. Maimakon abin ya ragu sai gashi ya koma wasu manyan hanyoyin wasu bangarorin kasar nan.

An ruwaito cewa, Babban Sufeton ‘Yansanda, Usman Baba ya ba jammi’ansa umarnin kasancewa a kan manyan hanyoyinmu musamman babbar hanyar Legas zuwa Ibadan don dakile karuwar ayyukan ‘yan ta’addan.

Bayanin jami’in yada labarai na rundunar, CSP Olumuyiwa Adejobi, ya nuna cewa, Babban Sufeton ya neni a sake fasalin ayyukan jami’an tsaron da ke aiki a manyan hanyoyinmu ta hanyar kai issasun jami’ai da kayan aiki don kare rayuka da dukiyoyin al’umma a wannan lokacin.

Ya kamata a ‘yansanda su dauki matakin da suka kamata na kare rayukan ‘yan Nijeriya wadanda babban laifinsu shi ne kasancewa a kan hanyoyin Nijeriya suna zirga-zirgar neman halaliyarsu. Bai kamata tafiya a kan hanyoyimmu ta zama mai hadari ba in har jammi’an tsaron da ke kan manyan hyanyoyimu suna gudanar da ayyukansu yadda ya kamata. ‘Yan Nijeriya da dama na fuskantar zabin dukiyarsu ko kuma rayuwarsu, wannan na faruwa ne ba kawai don ayyukan ‘yan bindiga ba kawai harma da yadda jami’an tsaron suka yi watsi da ayyukansu na kare aukuwar ayyukan ‘yanta’adda.

‘Yanuwan wadanda aka yi garkuwa da su kan kai ga sayar da kaddarorinsu masu muhimmanci don biyan kudaden fansa don ceto ‘yanuwan nasu daga hannun ‘yan bindiga.

Manyan hayoyinmu na da matukar muhimmanci ba kawai a bangaren tattalin arziki ba kawai har ma don dorewar harkar siyasar kasar nan, a kan haka ya zama dole gwamnati ta dauki harkar tsaron rayuwa da dukiyoyinmu da matukar muhimmanci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Tsare Wata Mata Kan Zargin Kashe ‘Yar Aikinta 

Next Post

CMG Ya Fitar Da Shirin “Shawarar Daukar Matakin Neman Bunkasuwa Na 2022” A Shafin Yanar Gizo

Related

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

5 days ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

6 days ago
Fyade
Rahotonni

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

2 weeks ago
APC
Manyan Labarai

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

2 weeks ago
Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Sanar Da Dakatar Da Ayyukanta Saboda Alhinin Rasuwar Buhari
Labarai

Na Shiga Aikin Soja Domin Gujewa Yin Auren Fari Da Ƙuruciya — Buhari

3 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

3 weeks ago
Next Post
CMG Ya Fitar Da Shirin “Shawarar Daukar Matakin Neman Bunkasuwa Na 2022” A Shafin Yanar Gizo

CMG Ya Fitar Da Shirin “Shawarar Daukar Matakin Neman Bunkasuwa Na 2022” A Shafin Yanar Gizo

LABARAI MASU NASABA

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu

July 31, 2025
Dangote Ya Bada Shawarar Samar Da Gidaje Masu Rahusa Da ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Mallaka

Dangote Ya Bada Shawarar Samar Da Gidaje Masu Rahusa Da ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Mallaka

July 31, 2025
NIN-SIM: Masu Hulda Da Kamfanonin Sadarwa Sun Koka Kan Katse Layinsu Daga Tsarin Kira

Kamfanonin Sadarwa Za Su Ci Gaba Da Rajistar Sabon SIM – NIMC

July 31, 2025
Matsayar Bai Daya Da Sin Da Amurka Suka Cimma Ta Fuskar Haraji Na Da Babbar Ma’ana

Matsayar Bai Daya Da Sin Da Amurka Suka Cimma Ta Fuskar Haraji Na Da Babbar Ma’ana

July 31, 2025
Mutane 44 Suka Mutu Bayan Mamakon Ruwa Da Aka Tafka A Beijing

Mutane 44 Suka Mutu Bayan Mamakon Ruwa Da Aka Tafka A Beijing

July 31, 2025
Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato

Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato

July 31, 2025
Zargin Da Wasu ’Yan Siyasar Amurka Ke Yi Wa Sin Na Fitar Da Hajoji Fiye Da Kima Ya Sabawa Hujjoji Na Hakika

Zargin Da Wasu ’Yan Siyasar Amurka Ke Yi Wa Sin Na Fitar Da Hajoji Fiye Da Kima Ya Sabawa Hujjoji Na Hakika

July 31, 2025
Gwamnatin Borno Ta Nada Kwamitin Aiwatar Da Mafi Karancin Albashi

Gwamna Zulum Ya Sauke Kwamishinoni Biyu Tare Da Maye Gurbinsu Da Wasu

July 31, 2025
Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka

Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka

July 31, 2025
Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

July 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.