ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Kara Tsaurara Tsaro A Hanyoyinmu

by Bello Hamza
4 years ago
Tsaro

A watan Janairu na wannan shekarar aka samu rahoton garkuwa da mutane a kan babbar hanyar Legas zuwa Ibadan. Hanyar ta kasance hanyar data fi daukar zirga-zirgar motoci a kasar nan, tana daukar mutane da kayyaki daga Arewaci zuwa Kudancin kasar nan.

A wani hari da ‘yan bindiga suka kai kwanan nan a daidai kauyen Abule Onigari inda suka kashe wani Direban motar haya, suka kuma yi awon gaba da fasinjoji 5. Kwana daya bayan nan kuma a daidai wurin da aka yina baya sai gashi ‘yan bindigan sun sake kai hari inda suka sace wata fittaciyar ‘yar fim mai suna, Bimpe Akintunde da ‘yarta. Tun daga wannan lokacin kuma sai rahottanin garkuwa da mutane a kan wannan babbar hanyar da ke da magtukar muhimmanci a zirga-zirgar mutane da kayyaki a tsakanin Arewaci da Kudancin Nijeriya ya cigaba da karuwa.

  • Gwamnatin Ebonyi Ta Ba Da Umarnin Kashe Duk Wanda Aka Gani Da Bindiga 

Matafiya da dama ciki har da Tsohon Mataimakin Shugaban Jami’ar Ibadan Farfesa Adigun Agbaje da wasu dalibai sun shiga hannun masu garkuwa da mutane a ranar 28 ga watan Oktoba, an sako ne bayan da aka biya wasu makudan kudade. Bayani ya nuna cewa, yawancin masu garkuwa da mutane na shigar sojoji ne yayin gudanar da ayyukansu.

ADVERTISEMENT

Rahoton ‘yansanda ya nuna cewa, an kai harin ne a kusa da Jami’ar Dominion da ke a bangare na karshen babbar hanyar Legas zuwa Ibadan, ‘yansanda sun bayyana yadda suka kai daukin gaggawa a karkashin jagorancin babban jami’in ‘yansanda na yankin, DPO da ‘yansanda Mobayil da gungun mafarauta suka kai daukin ceto mutanen a inda daya daga cikin ‘yansandan ya rasa ransa wasu kuma suka ji munanan raunuka, suna asibiti a halin yanzu suna karbar magani.

Yawaitar faruwar wannan ya fara zama wani kalubale ga mahukunta a halin yanzu. Haka kuma bayani ya nuna cewa, ‘yanbindigar na sanye ne da cikakkun kayan sojoji a yayin da suka datse hanyar. Abin lura a nan shi ne ayyukan wadannan ‘yan ta’addar ba su bar kowa ba a kan hanyoyin namu. In har wannan hare-haren suka ci gaba za su haifar da asarar rayuka da dukiyoyin al’umma masu dinbin yawa.

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

Amma ba wai a kan hanyoyinmu ne kadai ake fuskantar wannan barazanar ba. Kwanakin baya a cikin watan Yuni, an yi garkuwa da jami’a 10 na rundunar ‘yansandan Jihar Nasarawa a kan hanyarsu ta dawowa daga aikin sa ido a zaben gwamnan jihar Osun har zuwa wannan lokacin babu wani duriyar su. Bayani ya nuna cewa, an sace ‘yansandan ne a garin Obajana na Jihar Kogi a ranar 17 ga watan Yuli 2022, a daidai wurin da tireloli ke farkin da ake kira da ‘PTI Obajana’.

A daidai wannan lokacin na shekara da zirga-zirgar abin hawa ke kara karuwa, lokacin ne kuma da harkokin ‘yan ta’adda ke kaiwa makura. Kuma abubuwan kenan da ke faruwa a manyan hanyoyinmu a fadin tarayyar kasar nan.

Tuni ‘yan Nijeriya suka fara mantawa da kirga yawan garkuwa da mutanen da ake yi a kan babbar hanyar Abuja zuwa Kaduna dama hanyar Birnin Gwari zuwa Kaduna. Kasar bata kai ga farfadowa daga garkuwan da aka yi wa fasinjojin jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna ba, inda wadanda aka yi garkuwa da su suka yi fiye da watannin 8 a hannun ‘yan bindiga.

Ana zargin an biya ‘yan bindigan Billiyoyin Naira a mastayin kudin fansa kafin a kai ga sako kashi na karshe na mutanen kwanan nan. A yau babu wani magana a kan gudanar da cikakken bincike ballatana a kai ga hukunta wadanda suka aikata wannan laifin. Maimakon abin ya ragu sai gashi ya koma wasu manyan hanyoyin wasu bangarorin kasar nan.

An ruwaito cewa, Babban Sufeton ‘Yansanda, Usman Baba ya ba jammi’ansa umarnin kasancewa a kan manyan hanyoyinmu musamman babbar hanyar Legas zuwa Ibadan don dakile karuwar ayyukan ‘yan ta’addan.

Bayanin jami’in yada labarai na rundunar, CSP Olumuyiwa Adejobi, ya nuna cewa, Babban Sufeton ya neni a sake fasalin ayyukan jami’an tsaron da ke aiki a manyan hanyoyinmu ta hanyar kai issasun jami’ai da kayan aiki don kare rayuka da dukiyoyin al’umma a wannan lokacin.

Ya kamata a ‘yansanda su dauki matakin da suka kamata na kare rayukan ‘yan Nijeriya wadanda babban laifinsu shi ne kasancewa a kan hanyoyin Nijeriya suna zirga-zirgar neman halaliyarsu. Bai kamata tafiya a kan hanyoyimmu ta zama mai hadari ba in har jammi’an tsaron da ke kan manyan hyanyoyimu suna gudanar da ayyukansu yadda ya kamata. ‘Yan Nijeriya da dama na fuskantar zabin dukiyarsu ko kuma rayuwarsu, wannan na faruwa ne ba kawai don ayyukan ‘yan bindiga ba kawai harma da yadda jami’an tsaron suka yi watsi da ayyukansu na kare aukuwar ayyukan ‘yanta’adda.

‘Yanuwan wadanda aka yi garkuwa da su kan kai ga sayar da kaddarorinsu masu muhimmanci don biyan kudaden fansa don ceto ‘yanuwan nasu daga hannun ‘yan bindiga.

Manyan hayoyinmu na da matukar muhimmanci ba kawai a bangaren tattalin arziki ba kawai har ma don dorewar harkar siyasar kasar nan, a kan haka ya zama dole gwamnati ta dauki harkar tsaron rayuwa da dukiyoyinmu da matukar muhimmanci.

Tsaro
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba

MASU ALAKA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Rahotonni

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Next Post
CMG Ya Fitar Da Shirin “Shawarar Daukar Matakin Neman Bunkasuwa Na 2022” A Shafin Yanar Gizo

CMG Ya Fitar Da Shirin “Shawarar Daukar Matakin Neman Bunkasuwa Na 2022” A Shafin Yanar Gizo

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.