ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Kara Tsaurara Tsaro A Hanyoyinmu

by Bello Hamza
4 years ago
Tsaro

A watan Janairu na wannan shekarar aka samu rahoton garkuwa da mutane a kan babbar hanyar Legas zuwa Ibadan. Hanyar ta kasance hanyar data fi daukar zirga-zirgar motoci a kasar nan, tana daukar mutane da kayyaki daga Arewaci zuwa Kudancin kasar nan.

A wani hari da ‘yan bindiga suka kai kwanan nan a daidai kauyen Abule Onigari inda suka kashe wani Direban motar haya, suka kuma yi awon gaba da fasinjoji 5. Kwana daya bayan nan kuma a daidai wurin da aka yina baya sai gashi ‘yan bindigan sun sake kai hari inda suka sace wata fittaciyar ‘yar fim mai suna, Bimpe Akintunde da ‘yarta. Tun daga wannan lokacin kuma sai rahottanin garkuwa da mutane a kan wannan babbar hanyar da ke da magtukar muhimmanci a zirga-zirgar mutane da kayyaki a tsakanin Arewaci da Kudancin Nijeriya ya cigaba da karuwa.

  • Gwamnatin Ebonyi Ta Ba Da Umarnin Kashe Duk Wanda Aka Gani Da Bindiga 

Matafiya da dama ciki har da Tsohon Mataimakin Shugaban Jami’ar Ibadan Farfesa Adigun Agbaje da wasu dalibai sun shiga hannun masu garkuwa da mutane a ranar 28 ga watan Oktoba, an sako ne bayan da aka biya wasu makudan kudade. Bayani ya nuna cewa, yawancin masu garkuwa da mutane na shigar sojoji ne yayin gudanar da ayyukansu.

ADVERTISEMENT

Rahoton ‘yansanda ya nuna cewa, an kai harin ne a kusa da Jami’ar Dominion da ke a bangare na karshen babbar hanyar Legas zuwa Ibadan, ‘yansanda sun bayyana yadda suka kai daukin gaggawa a karkashin jagorancin babban jami’in ‘yansanda na yankin, DPO da ‘yansanda Mobayil da gungun mafarauta suka kai daukin ceto mutanen a inda daya daga cikin ‘yansandan ya rasa ransa wasu kuma suka ji munanan raunuka, suna asibiti a halin yanzu suna karbar magani.

Yawaitar faruwar wannan ya fara zama wani kalubale ga mahukunta a halin yanzu. Haka kuma bayani ya nuna cewa, ‘yanbindigar na sanye ne da cikakkun kayan sojoji a yayin da suka datse hanyar. Abin lura a nan shi ne ayyukan wadannan ‘yan ta’addar ba su bar kowa ba a kan hanyoyin namu. In har wannan hare-haren suka ci gaba za su haifar da asarar rayuka da dukiyoyin al’umma masu dinbin yawa.

LABARAI MASU NASABA

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

Amma ba wai a kan hanyoyinmu ne kadai ake fuskantar wannan barazanar ba. Kwanakin baya a cikin watan Yuni, an yi garkuwa da jami’a 10 na rundunar ‘yansandan Jihar Nasarawa a kan hanyarsu ta dawowa daga aikin sa ido a zaben gwamnan jihar Osun har zuwa wannan lokacin babu wani duriyar su. Bayani ya nuna cewa, an sace ‘yansandan ne a garin Obajana na Jihar Kogi a ranar 17 ga watan Yuli 2022, a daidai wurin da tireloli ke farkin da ake kira da ‘PTI Obajana’.

A daidai wannan lokacin na shekara da zirga-zirgar abin hawa ke kara karuwa, lokacin ne kuma da harkokin ‘yan ta’adda ke kaiwa makura. Kuma abubuwan kenan da ke faruwa a manyan hanyoyinmu a fadin tarayyar kasar nan.

Tuni ‘yan Nijeriya suka fara mantawa da kirga yawan garkuwa da mutanen da ake yi a kan babbar hanyar Abuja zuwa Kaduna dama hanyar Birnin Gwari zuwa Kaduna. Kasar bata kai ga farfadowa daga garkuwan da aka yi wa fasinjojin jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna ba, inda wadanda aka yi garkuwa da su suka yi fiye da watannin 8 a hannun ‘yan bindiga.

Ana zargin an biya ‘yan bindigan Billiyoyin Naira a mastayin kudin fansa kafin a kai ga sako kashi na karshe na mutanen kwanan nan. A yau babu wani magana a kan gudanar da cikakken bincike ballatana a kai ga hukunta wadanda suka aikata wannan laifin. Maimakon abin ya ragu sai gashi ya koma wasu manyan hanyoyin wasu bangarorin kasar nan.

An ruwaito cewa, Babban Sufeton ‘Yansanda, Usman Baba ya ba jammi’ansa umarnin kasancewa a kan manyan hanyoyinmu musamman babbar hanyar Legas zuwa Ibadan don dakile karuwar ayyukan ‘yan ta’addan.

Bayanin jami’in yada labarai na rundunar, CSP Olumuyiwa Adejobi, ya nuna cewa, Babban Sufeton ya neni a sake fasalin ayyukan jami’an tsaron da ke aiki a manyan hanyoyinmu ta hanyar kai issasun jami’ai da kayan aiki don kare rayuka da dukiyoyin al’umma a wannan lokacin.

Ya kamata a ‘yansanda su dauki matakin da suka kamata na kare rayukan ‘yan Nijeriya wadanda babban laifinsu shi ne kasancewa a kan hanyoyin Nijeriya suna zirga-zirgar neman halaliyarsu. Bai kamata tafiya a kan hanyoyimmu ta zama mai hadari ba in har jammi’an tsaron da ke kan manyan hyanyoyimu suna gudanar da ayyukansu yadda ya kamata. ‘Yan Nijeriya da dama na fuskantar zabin dukiyarsu ko kuma rayuwarsu, wannan na faruwa ne ba kawai don ayyukan ‘yan bindiga ba kawai harma da yadda jami’an tsaron suka yi watsi da ayyukansu na kare aukuwar ayyukan ‘yanta’adda.

‘Yanuwan wadanda aka yi garkuwa da su kan kai ga sayar da kaddarorinsu masu muhimmanci don biyan kudaden fansa don ceto ‘yanuwan nasu daga hannun ‘yan bindiga.

Manyan hayoyinmu na da matukar muhimmanci ba kawai a bangaren tattalin arziki ba kawai har ma don dorewar harkar siyasar kasar nan, a kan haka ya zama dole gwamnati ta dauki harkar tsaron rayuwa da dukiyoyinmu da matukar muhimmanci.

Tsaro
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Jihar Kano Za Ta Amfana Matuka Da Gidauniyar Aliko Dangote – Masu Ruwa Da Tsaki
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Nuna Damuwa Kan Sake Kamun Da DSS Ta Yi Wa Boɗejo Bayan Samun Belin EFCC
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Al’ummar Arewa Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani —Alfa Musa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ba Mu Taba Biyan Kudin Fansa Ba Kuma Ba Za Mu Biya Ba – Kwamishinan Katsina

MASU ALAKA

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Umarnin Kawo Karshen Matsalar Tsaro
Rahotonni

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

September 5, 2026
Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
Rahotonni

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

September 5, 2026
Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
Rahotonni

Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki

September 5, 2026
Next Post
CMG Ya Fitar Da Shirin “Shawarar Daukar Matakin Neman Bunkasuwa Na 2022” A Shafin Yanar Gizo

CMG Ya Fitar Da Shirin “Shawarar Daukar Matakin Neman Bunkasuwa Na 2022” A Shafin Yanar Gizo

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.