• English
  • Business News
Monday, September 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗan Takarar Gwamnan NNPP A Katsina Zai Kawar Da Ƙazantar APC Da PDP – Hajiya Farida Barau

by yahuzajere
3 years ago
in Siyasa
0
Ɗan Takarar Gwamnan NNPP A Katsina Zai Kawar Da Ƙazantar APC Da PDP – Hajiya Farida Barau
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Uwargidan ɗan takarar Gwamnan Jihar Katsina a Jam’iyyar NNPP, Engr Nura Khalil, wato Hajiya Farida Muhammad Barau ta bayyana cewa duk mutanen da ke cikin jam’iyyar NNPP mutanen kirki ne da ba su taɓa ɗaukar alhakin kowa a siyasa ba.

Uwargidan ɗan takarar rar ta bayyana hakan ne a ofishin yaƙin neman zaɓen maigidan nata da ke kan titin IBB Way cikin birnin Katsina, lokacin da ta ƙaddamar da muhimman manufofin takararsa ga matan jihar Katsina.

Hajiya Farida Muhammad Barau ta yi bayanin cewa ce; “Lema ta yage, tsintsiya ta watse, an ɗora mana yunwar dole, an sa mana talauci, mai cin abinci sau uku yanzun ma babu, an maida mu jawarawa, an kashe mana mazajenmu, an sace mana mata, shin wai haka za mu zauna ne?

“Mun zama shanaye an maida mu awakai, wannan Jam’iyya ta NNPP jaririya ce ba ta da hakkin kowa wallahi, mutanen duk da kuka gani cikin wannan jam’iyar mutanen kirki ne. Engr Muhammad Nura Khalil ya daɗe yana taimako, mai tausayi ne da kuɗinsa yake amfani yake fiddawa ya ba da, bai taɓa riƙe ko kansila ba, amma ya san hanyar da ake neman kuɗi, kuma a cikinsa yake ɗiba yake taimakon mutane.

“Shin ina ga ya samu wata dama wadda zai taimake ku da kuɗinku? Mine ne ba zai maku ba? Bai iya cin haƙƙin mutane ba, bai taɓa aikin gwamnati ba, bai taɓa ciyar da iyalinsa da haramun ba, bugu da ƙari ga shi yana da tausayin mata da ƙananan yara da matasa.” In ji Hajiya Farida.

Labarai Masu Nasaba

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

  • Da Dumi-dumi: Gwamnan Gombe Ya Rushe Shugabannin Kananan Hukumomin Bayan Karewar Wa’adin Mulkinsu

Har ila yau, shi ma a nasa jawabin, ɗan takarar gwamnan na NNPP a Jihar Katsina, Engr Muhammad Nura Khalil ya bayyana cewa idan ya lashe zaɓen jihar matan Katsina za su ji daɗi sosai, inda ya ƙara da cewa duk wata sai ya tallafi matan jihar Katsina dubu talatin da huɗu da kayan tallafi kuma har ya kammala wa’adinsa ba zai daina ba.

NNPP

Haka zalika da yake tofa albarkacin bakinsa, shugaban jam’iyyar NNPP ta Jihar katsina Honorable Sani Liti Yankwani ya yaba ma uwargidan dantakarar gwamnan a bisa ƙoƙarin da take na ganin maigidanta ya samu nasara da ma jam’iyya baki ɗaya, a zaɓe mai zuwa na 2023.

Ya ƙara da cewa babu shakka duk inda ka ga namiji ya samu nasara to za ka same shi da mace irin Hajiya Farida Muhammad Barau a tare da shi domin ita mace ce mai nagarta da kuma sanin ya kamata, “kazalika idan ba ka zauna da Farida ba ba za ka san wace ce Farida ba domin mace ce mai son ganin ci gaban Jihar Katsina da ma ƙasa baki ɗaya.”
Shi ma a nasa jawabin, Kwamrad Bashir Bala Funtua, ɗaya daga cikin matasan da ke dafa wa ɗan takarar na NNPP, Engr Nura Khalil baya wajen fafutukar jawo matasa don mara masa, ya bayyana cewa “ka da wata mace a Jihar Katsina ta yarda wasu ‘yan siyasa su ba su ‘yan kudi ƙalilan don zaɓar su, su tsaya su dubi cancanta su mara wa Engr Nura Khalil baya don samun kyakkyawan shugabanci a jihar Katsina.” In ji shi

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kungiyoyin Cinikayya Na Sin Sun Tafi Waje Don Neman Jari

Next Post

Yarjejeniyar Kare Mabambanta Hallitu a Duniya Ta Kunming Da Montreal Ta Fidda Wata Hanya Mai Dacewa a Fannin Kare Hallitu

Related

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa
Siyasa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

1 day ago
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC
Siyasa

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

2 days ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Siyasa

Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Sake Lashe Zaɓe A 2027 – Jigon APC

5 days ago
2027: Fastocin Takarar Shugaban Ƙasa Na Gwamnan Bauchi Sun Bayyana
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Gargaɗi Magoya Bayan Wike A PDP

5 days ago
Ina Da Yaƙinin Tinubu Ne Zai Lashe Zaɓen 2027 — Wike
Siyasa

Ina Da Yaƙinin Tinubu Ne Zai Lashe Zaɓen 2027 — Wike

7 days ago
Ɗaukar Nauyin Ƴan Ta’addan Da Suka Farmake Mu A Kaduna Aka Yi – El-Rufai
Siyasa

Ɗaukar Nauyin Ƴan Ta’addan Da Suka Farmake Mu A Kaduna Aka Yi – El-Rufai

7 days ago
Next Post
Yarjejeniyar Kare Mabambanta Hallitu a Duniya Ta Kunming Da Montreal Ta Fidda Wata Hanya Mai Dacewa a Fannin Kare Hallitu

Yarjejeniyar Kare Mabambanta Hallitu a Duniya Ta Kunming Da Montreal Ta Fidda Wata Hanya Mai Dacewa a Fannin Kare Hallitu

LABARAI MASU NASABA

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

September 7, 2025
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

September 7, 2025
Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

September 7, 2025
El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

September 7, 2025
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

September 7, 2025
An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

September 7, 2025
Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

September 7, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

September 7, 2025
NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

September 7, 2025
Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.