• English
  • Business News
Thursday, June 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NDLEA Ta Kwace Miyagun Kwayoyi Na Biliyan 450 A Wata 22 – Buba Marwa

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Rahotonni
0
NDLEA Ta Kwace Miyagun Kwayoyi Na Biliyan 450 A Wata 22 – Buba Marwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar hana sha da safarar miyagun kwayoyi (NDLEA) ta kwace miyagun kwayoyi da kudinsu ya kai kimanin naira biliyan 450 tare da damke masu safarar kwayoyi guda 23,907 a tsakanin watan Janairun 2021 zuwa watan Oktobar 2022.

Shugaban hukumar NDLEA, Buba Marwa shi ya bayyana hakan a warin bikin karramawa na karshen shekara da bayar da lambar yabo da kara wa jami’ai girma, wanda ya gudana a harabar shalkwatar hukumar NDLEA da ke Abuja.

  • INEC Za Ta Dauki Hayar Motocin Sufuri 100,000 Da Jiragen Ruwa 4,200 Don Raba Kayan Zabe – Yakubu
  • Da Dumi-Dumi: Saudiyya Ta Bai Wa Nijeriya Gurbin Mahajjata 95,000 A Hajji Mai Zuwa

Ya kara da cewa a lokacin gudanar da wannan bincike, hukumarsa ta samu nasarar cafke masu safarar miyagun kwayoyi guda 23,907 ciki har da hodar Iblis 29.

 “Mun kwace sama da tan miliyan 5,500 ko kilogiram miliyan 5.5 na miyagun kwayoyi wanda tsabar kudinsu ya sama da biliyan 450.

“A wannan lokacin dai, mun lalata konar wiwi da ta kai eka 772.5.

Labarai Masu Nasaba

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

“A cikin watanni 22, mun samu nasarar gurfanar da masu laifi har guda 3,434 a gaban kuliya.

“A konarinmu na yakin da miyagun kwayoyi, mun samu nasarar gyara tunanin mutum 16,114 wadanda suka kasance suna ta’ammuli da miyagun kwayoyi,” in ji shi.

Ya kara da cewa ayyukan da hukumarsa ta yi a tsawan watanni 22 ya dace ta gudanar da irin wannan biki.

Marwa ya ce wannan alkaluma da aka bayyan kididdiga ne kwai sai mutum ya yi nazari zai iya ganin irin cutarwar da suke yi wa al’umma. Ya ce za su yi matukar illa ga lafiya da kuma tsaro idan har aka bari wadannan miyagun kwayoyi suka shiga kan hanya.

A cewarsa, hukumar NDLEA ta kwace kwayar tiramado miliyan 100, ya ce idan har da wadannan kwayoyi sun kai ga kan hanyoyi, za su isa hannun masu sayarwa wanda babban illa ce ga al’umma.

“Wannan lamari yana da matukar matsala ga rayuwa, iyali da harkokin samarwa, saboda suna matukar illa ga matasa wanda su ne kashin bayan samar da kowani abu a kasar nan.

“Mun yi wannan nazari ne domin mu bayar da lambar yabo da karrama da karin matsayi bisa irin namijin kokarin da jami’anmu suka gudanar,” in ji shi.

Da yake mika lambar yabo da takardun karin girma ga jami’an NDLEA, Marwa ya bukaci su rike wannan lambar yabo a matsayin wasiyyar kwarewa na samun nasara.

Ya ce, “NDLEA za ta ci gaba da karrama wadanda suka bayar da gagarumar gudummuwa ga hukumar. Mun karrama jami’ai guda 3,506 a shekarar da ta gabata kuma ba nan za mu tsaya ba.

Marwa ya ce karin girma ya kasance lada ne na hukuma wanda take bayarwa ga gwarazan da suka nuna bajinta lokacin gudanar da ayyukansu. Ya ce ana bayar da shi ne ga wadanda suka cancanta kadai saboda su kara jajircewa wajen gudanar da ayyukan da aka dora musu.

Haka kuma ya ci gaba da cewa ba kowani jami’i ba ne ya cancanci a kara masa girma daga mukamin da ya kasance zuwa wani mukami na sama, sai dai wadanda suka cancanta ne kadai suke samun wannan dama.

Hukumar NDLEA ta kara wa jami’anta girma har guda 1,018, wadanda suka hada da manyan mataimakan kwamandoji guda da biyu. Haka kuma an kara wa jami’ai 17 da aka ba su sabon mukami na manyan mataimakan kwamandoji masu yaki da miyagun kwayoyi da kwamandoji 29 da matsakaitan mataimakan kwamandoji 78 da kuma sauran kananan mataimakan kwamandoji 111.

Sauran sun hada da babban sufuritanda 63 da sufuritanda 106 da kuma mataimakan sufuritanda 129. Akwai kuma wasu jami’ai guda 25 da aka ba su mukaman mataimakan sufuritanda na daya da kuma mataimakan sufuritanda na biyu guda 400.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Buba MarwaMiyagun KwayoyiNDLEARahoto
ShareTweetSendShare
Previous Post

“Ba Zamu Raba Wa Mata Da Matasa Akuyoyi Da Sunan Tallafin Sana’a Ba A Bauchi” —Sadique

Next Post

Banda Akwai Doka Da Mun Shiga Gidan Gwamnatin Bauchi Mun Kwato Mulkinmu —Adamu

Related

NDLEA
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

5 days ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

6 days ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

2 weeks ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

2 weeks ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

3 weeks ago
Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

2 months ago
Next Post
Banda Akwai Doka Da Mun Shiga Gidan Gwamnatin Bauchi Mun Kwato Mulkinmu —Adamu

Banda Akwai Doka Da Mun Shiga Gidan Gwamnatin Bauchi Mun Kwato Mulkinmu —Adamu

LABARAI MASU NASABA

Yadda Kasar Sin Ta Zo Da Sabon Salon Zamanantar Da Sashen Jigilar Kayayyaki

Yadda Kasar Sin Ta Zo Da Sabon Salon Zamanantar Da Sashen Jigilar Kayayyaki

June 11, 2025
haraji

Tinubu Ya Soke Yin Jawabi Ga ‘Yan Kasa Na Ranar Dimokuradiyya, Zai Yi Daga Zauren Majalisa

June 11, 2025
An Gudanar Da Taron Ministoci Masu Daidaita Ayyukan Da Aka Amince Yayin Taron FOCAC

An Gudanar Da Taron Ministoci Masu Daidaita Ayyukan Da Aka Amince Yayin Taron FOCAC

June 11, 2025
Dangote

Ɗan Ƙasar Indiya Da Wasu 12 Sun Gurfana A Kotu Kan Satar Wa Dangote Dizal Na Naira Biliyan 4

June 11, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Kaso Kusan 80% Sun Soki Musabbabin Barkewar Tarzoma A Amurka

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Kaso Kusan 80% Sun Soki Musabbabin Barkewar Tarzoma A Amurka

June 11, 2025
Kasuwancin Sin Da Afirka Ya Habaka Cikin Hanzari A Shekaru 25 Da Suka Gabata

Kasuwancin Sin Da Afirka Ya Habaka Cikin Hanzari A Shekaru 25 Da Suka Gabata

June 11, 2025
Filato

‘Yan Bindiga Sun Sake Kashe Mutane 8 A Jihar Filato

June 11, 2025
He Lifeng Ya Bukaci Amurka Da Ta Warware Takaddamar Cinikayya Da Sin Ta Hanyar Tattaunawa Da Hadin Gwiwa

He Lifeng Ya Bukaci Amurka Da Ta Warware Takaddamar Cinikayya Da Sin Ta Hanyar Tattaunawa Da Hadin Gwiwa

June 11, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Afrika

Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Afrika

June 11, 2025
Duk Da Cewa Wike Ba Ɗan APC Ba Ne Amma Muna Jin Daɗin Aikin sa – Tinubu

Duk Da Cewa Wike Ba Ɗan APC Ba Ne Amma Muna Jin Daɗin Aikin sa – Tinubu

June 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.