ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NDLEA Ta Kwace Miyagun Kwayoyi Na Biliyan 450 A Wata 22 – Buba Marwa

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
NDLEA

Hukumar hana sha da safarar miyagun kwayoyi (NDLEA) ta kwace miyagun kwayoyi da kudinsu ya kai kimanin naira biliyan 450 tare da damke masu safarar kwayoyi guda 23,907 a tsakanin watan Janairun 2021 zuwa watan Oktobar 2022.

Shugaban hukumar NDLEA, Buba Marwa shi ya bayyana hakan a warin bikin karramawa na karshen shekara da bayar da lambar yabo da kara wa jami’ai girma, wanda ya gudana a harabar shalkwatar hukumar NDLEA da ke Abuja.

  • INEC Za Ta Dauki Hayar Motocin Sufuri 100,000 Da Jiragen Ruwa 4,200 Don Raba Kayan Zabe – Yakubu
  • Da Dumi-Dumi: Saudiyya Ta Bai Wa Nijeriya Gurbin Mahajjata 95,000 A Hajji Mai Zuwa

Ya kara da cewa a lokacin gudanar da wannan bincike, hukumarsa ta samu nasarar cafke masu safarar miyagun kwayoyi guda 23,907 ciki har da hodar Iblis 29.

ADVERTISEMENT

 “Mun kwace sama da tan miliyan 5,500 ko kilogiram miliyan 5.5 na miyagun kwayoyi wanda tsabar kudinsu ya sama da biliyan 450.

“A wannan lokacin dai, mun lalata konar wiwi da ta kai eka 772.5.

LABARAI MASU NASABA

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

“A cikin watanni 22, mun samu nasarar gurfanar da masu laifi har guda 3,434 a gaban kuliya.

“A konarinmu na yakin da miyagun kwayoyi, mun samu nasarar gyara tunanin mutum 16,114 wadanda suka kasance suna ta’ammuli da miyagun kwayoyi,” in ji shi.

Ya kara da cewa ayyukan da hukumarsa ta yi a tsawan watanni 22 ya dace ta gudanar da irin wannan biki.

Marwa ya ce wannan alkaluma da aka bayyan kididdiga ne kwai sai mutum ya yi nazari zai iya ganin irin cutarwar da suke yi wa al’umma. Ya ce za su yi matukar illa ga lafiya da kuma tsaro idan har aka bari wadannan miyagun kwayoyi suka shiga kan hanya.

A cewarsa, hukumar NDLEA ta kwace kwayar tiramado miliyan 100, ya ce idan har da wadannan kwayoyi sun kai ga kan hanyoyi, za su isa hannun masu sayarwa wanda babban illa ce ga al’umma.

“Wannan lamari yana da matukar matsala ga rayuwa, iyali da harkokin samarwa, saboda suna matukar illa ga matasa wanda su ne kashin bayan samar da kowani abu a kasar nan.

“Mun yi wannan nazari ne domin mu bayar da lambar yabo da karrama da karin matsayi bisa irin namijin kokarin da jami’anmu suka gudanar,” in ji shi.

Da yake mika lambar yabo da takardun karin girma ga jami’an NDLEA, Marwa ya bukaci su rike wannan lambar yabo a matsayin wasiyyar kwarewa na samun nasara.

Ya ce, “NDLEA za ta ci gaba da karrama wadanda suka bayar da gagarumar gudummuwa ga hukumar. Mun karrama jami’ai guda 3,506 a shekarar da ta gabata kuma ba nan za mu tsaya ba.

Marwa ya ce karin girma ya kasance lada ne na hukuma wanda take bayarwa ga gwarazan da suka nuna bajinta lokacin gudanar da ayyukansu. Ya ce ana bayar da shi ne ga wadanda suka cancanta kadai saboda su kara jajircewa wajen gudanar da ayyukan da aka dora musu.

Haka kuma ya ci gaba da cewa ba kowani jami’i ba ne ya cancanci a kara masa girma daga mukamin da ya kasance zuwa wani mukami na sama, sai dai wadanda suka cancanta ne kadai suke samun wannan dama.

Hukumar NDLEA ta kara wa jami’anta girma har guda 1,018, wadanda suka hada da manyan mataimakan kwamandoji guda da biyu. Haka kuma an kara wa jami’ai 17 da aka ba su sabon mukami na manyan mataimakan kwamandoji masu yaki da miyagun kwayoyi da kwamandoji 29 da matsakaitan mataimakan kwamandoji 78 da kuma sauran kananan mataimakan kwamandoji 111.

Sauran sun hada da babban sufuritanda 63 da sufuritanda 106 da kuma mataimakan sufuritanda 129. Akwai kuma wasu jami’ai guda 25 da aka ba su mukaman mataimakan sufuritanda na daya da kuma mataimakan sufuritanda na biyu guda 400.

NDLEA
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Umarnin Kawo Karshen Matsalar Tsaro
Rahotonni

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

September 5, 2026
Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
Rahotonni

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

September 5, 2026
Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
Rahotonni

Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki

September 5, 2026
Next Post
Banda Akwai Doka Da Mun Shiga Gidan Gwamnatin Bauchi Mun Kwato Mulkinmu —Adamu

Banda Akwai Doka Da Mun Shiga Gidan Gwamnatin Bauchi Mun Kwato Mulkinmu —Adamu

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.