ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NDLEA Ta Kwace Miyagun Kwayoyi Na Biliyan 450 A Wata 22 – Buba Marwa

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
NDLEA

Hukumar hana sha da safarar miyagun kwayoyi (NDLEA) ta kwace miyagun kwayoyi da kudinsu ya kai kimanin naira biliyan 450 tare da damke masu safarar kwayoyi guda 23,907 a tsakanin watan Janairun 2021 zuwa watan Oktobar 2022.

Shugaban hukumar NDLEA, Buba Marwa shi ya bayyana hakan a warin bikin karramawa na karshen shekara da bayar da lambar yabo da kara wa jami’ai girma, wanda ya gudana a harabar shalkwatar hukumar NDLEA da ke Abuja.

  • INEC Za Ta Dauki Hayar Motocin Sufuri 100,000 Da Jiragen Ruwa 4,200 Don Raba Kayan Zabe – Yakubu
  • Da Dumi-Dumi: Saudiyya Ta Bai Wa Nijeriya Gurbin Mahajjata 95,000 A Hajji Mai Zuwa

Ya kara da cewa a lokacin gudanar da wannan bincike, hukumarsa ta samu nasarar cafke masu safarar miyagun kwayoyi guda 23,907 ciki har da hodar Iblis 29.

ADVERTISEMENT

 “Mun kwace sama da tan miliyan 5,500 ko kilogiram miliyan 5.5 na miyagun kwayoyi wanda tsabar kudinsu ya sama da biliyan 450.

“A wannan lokacin dai, mun lalata konar wiwi da ta kai eka 772.5.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

“A cikin watanni 22, mun samu nasarar gurfanar da masu laifi har guda 3,434 a gaban kuliya.

“A konarinmu na yakin da miyagun kwayoyi, mun samu nasarar gyara tunanin mutum 16,114 wadanda suka kasance suna ta’ammuli da miyagun kwayoyi,” in ji shi.

Ya kara da cewa ayyukan da hukumarsa ta yi a tsawan watanni 22 ya dace ta gudanar da irin wannan biki.

Marwa ya ce wannan alkaluma da aka bayyan kididdiga ne kwai sai mutum ya yi nazari zai iya ganin irin cutarwar da suke yi wa al’umma. Ya ce za su yi matukar illa ga lafiya da kuma tsaro idan har aka bari wadannan miyagun kwayoyi suka shiga kan hanya.

A cewarsa, hukumar NDLEA ta kwace kwayar tiramado miliyan 100, ya ce idan har da wadannan kwayoyi sun kai ga kan hanyoyi, za su isa hannun masu sayarwa wanda babban illa ce ga al’umma.

“Wannan lamari yana da matukar matsala ga rayuwa, iyali da harkokin samarwa, saboda suna matukar illa ga matasa wanda su ne kashin bayan samar da kowani abu a kasar nan.

“Mun yi wannan nazari ne domin mu bayar da lambar yabo da karrama da karin matsayi bisa irin namijin kokarin da jami’anmu suka gudanar,” in ji shi.

Da yake mika lambar yabo da takardun karin girma ga jami’an NDLEA, Marwa ya bukaci su rike wannan lambar yabo a matsayin wasiyyar kwarewa na samun nasara.

Ya ce, “NDLEA za ta ci gaba da karrama wadanda suka bayar da gagarumar gudummuwa ga hukumar. Mun karrama jami’ai guda 3,506 a shekarar da ta gabata kuma ba nan za mu tsaya ba.

Marwa ya ce karin girma ya kasance lada ne na hukuma wanda take bayarwa ga gwarazan da suka nuna bajinta lokacin gudanar da ayyukansu. Ya ce ana bayar da shi ne ga wadanda suka cancanta kadai saboda su kara jajircewa wajen gudanar da ayyukan da aka dora musu.

Haka kuma ya ci gaba da cewa ba kowani jami’i ba ne ya cancanci a kara masa girma daga mukamin da ya kasance zuwa wani mukami na sama, sai dai wadanda suka cancanta ne kadai suke samun wannan dama.

Hukumar NDLEA ta kara wa jami’anta girma har guda 1,018, wadanda suka hada da manyan mataimakan kwamandoji guda da biyu. Haka kuma an kara wa jami’ai 17 da aka ba su sabon mukami na manyan mataimakan kwamandoji masu yaki da miyagun kwayoyi da kwamandoji 29 da matsakaitan mataimakan kwamandoji 78 da kuma sauran kananan mataimakan kwamandoji 111.

Sauran sun hada da babban sufuritanda 63 da sufuritanda 106 da kuma mataimakan sufuritanda 129. Akwai kuma wasu jami’ai guda 25 da aka ba su mukaman mataimakan sufuritanda na daya da kuma mataimakan sufuritanda na biyu guda 400.

NDLEA
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Banda Akwai Doka Da Mun Shiga Gidan Gwamnatin Bauchi Mun Kwato Mulkinmu —Adamu

Banda Akwai Doka Da Mun Shiga Gidan Gwamnatin Bauchi Mun Kwato Mulkinmu —Adamu

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.