• English
  • Business News
Thursday, June 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Kasar Sin Ke Tallafawa Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Yadda Kasar Sin Ke Tallafawa Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Har kullum shaidun gani da ido na kara tabbatar da aniyar kasar Sin ta gina alummar duniya mai makomar bai daya ga kowa, kuma tana ci gaba da bude kofa ga kasashen waje, da aiwatar da sauye-sauye masu inganci a gida, da gudanar da hadin gwiwa domin cin gajiyar juna tsakaninta da sauran kasashe, da aiwatar da manufofin bunkasar duniya baki daya.

Ko da a ’yan kwanakin baya bayan nan ma, sai dai jakadan Sin a Amurka Qin Gang ya kara nanata wadannan manufofi na kasar Sin, cikin wani sharhi da aka wallafa. Kuma hakan na zuwa ne a gabar da Sin din ke kara fuskantar suka daga wasu kasashen yammacin duniya, wadanda ke kallon kasar a matsayin barazana gare su, duk da ba sa iya gabatar da sahihan dalilai na tabbatar da zargin nasu.

  • Kasar Sin Ta Dage Ka’idojin Yaki Da COVID-19 Ga Matafiya Daga Ketare

Kafin hakan, yayin taron wakilan jamaa na jamiyyar kwaminis mai mulkin kasar Sin karo na 20 wanda ya gabata a watan Oktoba, mahukuntan kasar sun jaddada manufofin waje na kasar, manufofin da suka kunshi wanzar da zaman lafiya, da ingiza ci gaban duniya baki daya, yayin da take fatan gina alummar duniya mai makomar bai daya ga dukkanin bil adama.

Karkashin manufofin kara bude kofa ga waje, tuni kasar Sin ta kafa yankunan gwaji na cinikayya maras shinge har 21, tare da fadada yawan yarjejeniyoyin cinikayya cikin ’yanci daga 10 zuwa 19, ciki har da cikakkiyar yarjejeniyar hadin gwiwar raya tattalin arziki ta shiyya ko FTA, irinta mafi girma a duniya.

Yanzu haka karin kasashen duniya musamman masu tasowa, na cin gajiya daga babbar kasuwar kasar Sin, wanda hakan ya kara budewa kasashe masu tasowa kafofin shigar da hajojinsu zuwa kasuwannin Sin. Karkashin manufofinta na samar da gata ga kasashe masu tasowa, Sin ta dage harajin shigo da wasu hajoji daga wasu kasashe masu rauni, ta yadda za su kai ga bunkasa gajiyar da suke samu daga cudanya da kasar. A hannu guda Sin din ta cire karin wasu sassan zuba jari daga jerin sassan da a baya aka sanyawa shinge ga masu zuba jarin waje, daga sassan 93 a baya zuwa 31 a yanzu.

Labarai Masu Nasaba

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

Bugu da kari, wasu alkaluma da bankin duniya ya fitar sun nuna yadda kasuwannin Sin ke kara fadada, da janyo hankulan masu zuba jari. Alkaluman sun nuna yadda kasar Sin ta daga zuwa matsayi na 31, cikin jerin kasashe masu saukin gudanar da hada-hadar cinikayya a duniya, wanda hakan ya nuna cewa, kasar ta samu karin maki 65 cikin shekaru 10 da suka gabata a wannan fanni.

Idan kuma aka tabo batun tallafin wanzar da zaman lafiya, mun san cewa kasar Sin na kan gaba a duniya, a jerin kasashen dake samar da taikamo ga ayyukan wanzar da zaman lafiya na MDD, yayin da manufofinta na wanzar da ci gaba, da jure kalubalen da duniya ke ciki ta fukar raya tattalin arziki a gida, ke kara ingiza ci gaban tattalin arzikin duniya baki daya.

Duk da bambance-bambance dake tsakanin Sin da kasashe daban daban ta fuskar tarihi, aladu, zamantakewa da salon jagoranci. Masharhanta na cewa, kasancewar bil adama na rayuwa a duniya daya, kamata ya yi alummun duniya baki daya su rungumi akidun kasar Sin na kawar da sabani, da nunawa juna yatsa, ko mayar da wasu kasashe saniyar ware, ta yadda dukkanin sassan duniya za su mutunta juna, da bunkasa zaman lafiya, da cin gajiya tare, domin a tafi tare a tsira tare. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Dumi-Dumi: Gwarzon Dan Wasan Brazil Pele Ya Rasu

Next Post

Dan Wasan Duniya, Pele, Ya Rasu Yana Da Shekaru 82

Related

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai
Daga Birnin Sin

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

18 hours ago
Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

19 hours ago
Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba
Daga Birnin Sin

Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

20 hours ago
Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana
Daga Birnin Sin

Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

22 hours ago
Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 
Daga Birnin Sin

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

24 hours ago
Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

1 day ago
Next Post
Dan Wasan Duniya, Pele, Ya Rasu Yana Da Shekaru 82

Dan Wasan Duniya, Pele, Ya Rasu Yana Da Shekaru 82

LABARAI MASU NASABA

Malta Guinness

Bikin Bukin Sallar Da Malta Guinness

June 5, 2025
Hukumar kashe gobara

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

June 5, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

June 5, 2025
Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

June 5, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

June 5, 2025
Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

June 5, 2025
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

June 5, 2025
An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

June 5, 2025
Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

June 5, 2025
Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.