ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Ta Dage Ka’idojin Yaki Da COVID-19 Ga Matafiya Daga Ketare

by CMG Hausa
3 years ago
COVID-19

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta sanar a yau Talata cewa, daga ranar 8 ga watan Junairu, za a soke gwajin cutar COVID-19 ga matafiyan daga ketare.

Sanarwar da ma’aikatar harkokin wajen ta wallafa a shafinta na yanar gizo, ta ce ana shawartar masu zuwa kasar Sin daga ketare, su yi gwajin cutar sa’o’i 48 kafin lokacin tafiyarsu. Inda kuma ake shawartar wadanda gwaji ya nuna sun kamu da cutar, su jinkirta tafiyar zuwa lokacin da gwaji zai nuna ba sa dauke da ita.

  • Sin Tana Mai Da Moriyar Jama’a a Gaban Kome Yayin Da Take Aiwatar Da Matakan Yaki Da Cutar Covid-19

Haka kuma, babu bukatar matafiya su nemi manhajar tantance yanayin cutar ta Health Code, daga ofisoshin jakadancin kasar Sin.
A cewar sanarwar, za su bayyana yanayin lafiyarsu ne a katin da za su gabatarwa jami’an kwastam.

ADVERTISEMENT

Wadanda kuma yanayin lafiyarsu ke da matsala ko suke dauke da zazzabi, za su yi gwaji a wurin, sannan kuma za a nemi su killace kansu a gida ko su je asibiti, bisa la’akari da yanayin lafiyarsu.

A cewar sanarwar, kasar Sin za ta soke matakan takaitawa da ta sanya wa jiragen saman fasinja na kasa da kasa, inda za ta kara yawan zirga-zirgar jiragen sama bisa matakai, da inganta hanyoyin da jiragen ke bi.

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Bugu da kari, kamfanonin jiragen sama za su ci gaba da fesa maganin kashe kwayoyin cuta a cikin jiragensu, kuma ana bukatar fasinjoji su sanya abin rufe fuska da baki yayin da suke cikin jirgi.

Kasar Sin za ta kara inganta tsare-tsare ga baki da ke shigowa kasar Sin don yin aiki, kasuwanci, karatu, ziyara da haduwa da dangi, da samun viza cikin sauki yadda ya kamata.

Sanarwar ta kuma bayyana cewa, za a dauki matakan tabbatar da cewa, jigilar kayayyaki a tashoshin jiragen ruwa daban-daban, za su koma kamar yadda suke kafin barkewar cutar, kuma za a dawo da harkokin yawon bude ido ga ‘yan kasar Sin cikin tsari.

Wadannan sauye-sauye, sun yi daidai da ingantattun matakan rigakafin kamuwa da cutar a cikin gida, za kuma su daidaita matakan rigakafin annobar da sarrafawa tare da ci gaban tattalin arziki da zamantakewa da kuma sanya tafiye-tafiye tsakanin kasashe kan turba mafi dacewa, aminci, tsari da inganci.

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Wang Wenbin ya yi wadannan kalamai ne, a yayin taron manema labarai da aka saba shiryawa a Talatar nan, lokacin da aka tambaye shi game da sabbin matakan.

A kokarinta na sauya manufofinta kan cutar COVID-19, hukumar kula da lafiya ta kasar Sin ta fitar da wata sanarwa jiya Litinin, inda ta ce kasar Sin za ta sauya matakan yaki da cutar daga rukunin A zuwa rukunin B daga ranar 8 ga watan Junairu na shekarar 2023 dake tafe, tare da kuma sauyawa cutar suna daga “novel coronavirus pneumonia” wato matakin cutar mai tsanani dake shafar huhu, zuwa “novel coronavirus infection” bisa dokokin kandagarki da yaki da cutar, tare da cire ta daga jerin cututtukan dake bukatar killacewa, bisa dokokin kiwon lafiya da na killacewa na kasar.

Sawarwar da kwamitin kula da matakan kandagarki da dakile yaduwar cutar, na majalisar gudanarwar kasar Sin ya fitar a jiyan, ta ce an riga an dauki dukkan matakan da suka kamata, wadanda za su taimakwa wajen daidaita sassauta matakan, bisa dogaro da yanayin sauyawar cutar da kuma yadda ake tunkararta a kasar.

A waje daya kuma, kasar Sin ta kara daukar matakan kandagarki da dakile annobar COVID-19 a muhimman wurare, kungiyoyi da rukuninin jama’a, a daidai lokacin da kasar ta sauya matakanta na yaki da cutar COVID-19.

Muhimmiyar takardar, wadda kwamitin yaki da annobar na majalisar gudanarwar kasar ya fitar, ta lura cewa, ya kamata a kara adadin rigakafin da ake yiwa mutanen da ke zaune a wuraren kula da tsoffi da cibiyoyin jin dadin jama’a, yayin da mutane ke cikin hadarin ci gaba da shiga yanayi mai tsanani, ciki har da mutane masu shekaru 60 zuwa sama, mutanen da ke da wani rashin lafiya, da wadanda ba su da karin garkuwar jiki, aka shawarce su da su hanzarta karbar allurar dake kara karfin garkuwa. (Masu Fassarawa: Fa’iza Mustapha & Ibrahim Yaya)

COVID-19
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji
Daga Birnin Sin

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina
Daga Birnin Sin

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Mutan 3 Yankan Rago Da Sace Wasu Da Dama A Wani Sabon Hari A Neja

DA DUMI-DUMI: An Sace Mutum 16 A Wani Sabon Hari Da Aka Kai Jihar Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Sowore Ya Sha Alwashin Ci Gaba Da Gwagwarmaya Duk Da Tsare Shi A Gidan Yarin Kuje

Jagoran Matasan AAC Kwamret Yahaya Soje Ya Nemi A Saki Sowore

June 26, 2026
Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC

Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC

June 26, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

June 26, 2026
Noma

Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba

June 26, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

June 26, 2026
Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

June 26, 2026
Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

June 26, 2026
Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.