• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Bankado Maboyar IPOB A Ribas

by Sadiq
3 years ago
IPOB

Rundunar ‘yansandan Jihar Ribas ta ce ta kai samame aata maboyar ‘yan kungiyar Biyafara (IPOB) da ke karamar hukumar Oyigbo a jihar.

Kwamishinan ‘yansandan jihar, Okon Effiong ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a yayin da yake gabatar da wasu da ake zargi da aikata laifukan da ke alaka da ta’addanci a sassan jihar.

  • Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Jawabin Sabuwar Shekara Ga Majalissar CPPCC
  • Tawagar Jami’an Lafiya Sinawa Ta Shirya Horo Kan Kula Da Marasa Lafiya Dake Cikin Yanayi Mai Tsanani A Sudan

A cewar Effiong, akwai ‘yan kungiyar IPOB 10 da suka hada da wadanda aka kama da hannu wajen kona ofishin ‘yansanda na Oyigbo a lokacin zanga-zangar EndSARS.

Effiong wanda ya sha alwashin cewa rundunar ba za ta kyale duk wani nau’i na miyagun ayyuka a jihar ba, ya bayyana cewa bakwai daga cikin masu garkuwa da mutane takwas da suka yi garkuwa da shugaban wani kamfanin mai a gadar sama ta Rumuokoro sun kama su tare da kubutar da wanda suka sace.

Hakan dai na zuwa ne a lokacin da jami’an rundunar suka kai farmaki kan sansanin nasu da ke Omoku.

LABARAI MASU NASABA

Rundunar Sojin Sama Ta Kai Hari Kan ISWAP Da Ƴan Bindiga A Borno, Kwara Da Katsina

Sojoji Sun Fatattaki Boko Haram, Sun Ceto Mutane 86 Da Aka Sace A Borno

CP Effiong, wanda ya kara da cewa, sama da mutane 120 da ake zargi da aikata laifuka an kama su da laifuka daban-daban a fadin jihar, ya fitar da kididdigar kama mutanen, wadanda aka kama da kuma wadanda suka jikkata.

“An kama mutane 22 da ake zargi da yin garkuwa da mutane 27 da ‘yan fashi da makami yayin da aka kashe jami’an ‘yansanda uku a lokacin da ake bincike,” in ji shi.

Ya kara da cewa, an kwato makamai 21 da alburusai 136, an ceto mutane 11 da aka yi garkuwa da su, sannan jami’an sun lalata wuraren hada-hadar kudi guda hudu tsakanin Oktoba da Disamba 2022.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Rundunar Sojin Sama Ta Kai Hari Kan ISWAP Da Ƴan Bindiga A Borno, Kwara Da Katsina
Manyan Labarai

Rundunar Sojin Sama Ta Kai Hari Kan ISWAP Da Ƴan Bindiga A Borno, Kwara Da Katsina

November 10, 2025
Boko haram
Manyan Labarai

Sojoji Sun Fatattaki Boko Haram, Sun Ceto Mutane 86 Da Aka Sace A Borno

November 10, 2025
Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025
Next Post
Babban Layin Samar Da Wutar Lantarki Na Kasar Sin Ya Fara Aiki Gadan-Gadan

Babban Layin Samar Da Wutar Lantarki Na Kasar Sin Ya Fara Aiki Gadan-Gadan

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Taya Ouattara Murnar Sake Lashe Zaben Shugaban Cote D’Ivoire

Xi Ya Taya Ouattara Murnar Sake Lashe Zaben Shugaban Cote D’Ivoire

November 10, 2025
Rundunar Sojin Sama Ta Kai Hari Kan ISWAP Da Ƴan Bindiga A Borno, Kwara Da Katsina

Rundunar Sojin Sama Ta Kai Hari Kan ISWAP Da Ƴan Bindiga A Borno, Kwara Da Katsina

November 10, 2025
Xi Ya Halarci Bikin Bude Gasar Wasanni Ta Sin Karo Na 15 A Guangzhou

Xi Ya Halarci Bikin Bude Gasar Wasanni Ta Sin Karo Na 15 A Guangzhou

November 10, 2025
Gwamnatin Kaduna Za Ta Ɗauki Ma’aikatan Lafiya 9,000 Cikin Shekaru 5 – Maiyaki 

Gwamnatin Kaduna Za Ta Ɗauki Ma’aikatan Lafiya 9,000 Cikin Shekaru 5 – Maiyaki 

November 10, 2025
Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo

Wani Sabon Hari Kan Al’ummar Da Ke Iyaka Da Katsina A Kano Ya Rutsa Da Mata 5

November 10, 2025
Matatun mai

Yadda Sojoji Suka Tarwatsa Haramtattun Matatun Mai 14 A Yankin Neja Delta 

November 10, 2025
Jibrin Kofa

Ɗan Majalisar Wakilai, Jibrin Ƙofa Ya Sauya Sheƙa Daga NNPP Zuwa APC

November 10, 2025
Boko haram

Sojoji Sun Fatattaki Boko Haram, Sun Ceto Mutane 86 Da Aka Sace A Borno

November 10, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025
An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.