• English
  • Business News
Friday, July 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Tinubu Ya Fi Ni Koshin Lafiya – Shettima

by Sadiq
3 years ago
in Siyasa
0
2023: Tinubu Ya Fi Ni Koshin Lafiya – Shettima
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mataimakin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Kashim Shettima, ya bayyana cewa, Bola Tinubu, ya fi shi lafiya.

Shettima, ya bayyana haka ne a ranar Lahadi a wani shiri na kai-tsaye ta Facebook, mai taken “Fashin Baki”, wanda Bulama Bukarti, Nasir Zango, Abba Hikima da Jaafar Jaafar su ke shirya.

  • ‘Yansanda Sun Dakile Harin ‘Yan Bindiga Tare Da Bindige 1 A Jihar Katsina
  • Ministan Wajen Sin Ya Tattauna Da Takwaransa Na Amurka Ta Wayar Tarho

Jama’a na nuna damuwa kan yanayin lafiyar dan takarar na APC, inda wasu ke cewa bai cancanci zama shugaban kasa ba.

Sai dai Shettima, ya ce Tinubu ya ma fi shi lafiya domin ba shi da ciwon suga ko hawan jini.

“Bari na fada muku karara cewa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, mutum ne mai lafiya garau ya ke.

Labarai Masu Nasaba

Ko Kaɗan Bamu Ji Takaicin Ficewar Atiku Daga Jam’iyyar PDP Ba — Damagum

Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

“A ajiye siyasa a gefe, Tinubu na da lafiya a jiki da kuma karfin tunani da zai iya rike Nijeriya.

“Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya fi ni koshin lafiya kasancewar ni ina da ciwon suga da hawan jini, wanda shi kuma ba shi da shi.

Ko da ma cutar da mutane suka yi magana game da ita, rashin barci ne kawai. Da zarar ya samu isasshen barci, zai zama ya yi garau.

“Shugabanci ba kamar aikin karfi na daukar buhunan siminti ba ne. Yawanci aiki da kwakwalwa ya fi yawa a kan da jiki.

“Tsofaffin shugabannin kasa, Theodore Roosevelt da Abdelaziz Bouteflika da Daniel Arap Moi na Amurka da Algeria da Kenya sun jagoranci kasashensu ta hanyar bunkasar tattalin arziki yayin da suka dinga amfani da keken guragu,” in ji Shettima.

Tinubu ya sha suka kan yanayin lafiyarsa, lamarin da ya sanya abokan hammata ke masa adawa da lamarin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCKashim ShettimaLafiyaSiyasatakaraTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa Tsohon Gwamnan Imo Hari, Sun Kashe ‘Yansanda 4

Next Post

Wadanda Suka Kai Wa Ayarina Hari Za Su Dandana Kudarsu – Tambuwal

Related

Ko Kaɗan Bamu Ji Takaicin Ficewar Atiku Daga Jam’iyyar PDP Ba — Damagum
Labarai

Ko Kaɗan Bamu Ji Takaicin Ficewar Atiku Daga Jam’iyyar PDP Ba — Damagum

4 hours ago
Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC
Manyan Labarai

Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

1 day ago
PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde
Labarai

PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

2 days ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

5 days ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

1 week ago
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista
Manyan Labarai

Shugabannin Jam’iyyar ADC Na Jihohi 36 Da Abuja Sun Bayyana Goyon Bayansu Ga David Mark

1 week ago
Next Post
Wadanda Suka Kai Wa Ayarina Hari Za Su Dandana Kudarsu – Tambuwal

Wadanda Suka Kai Wa Ayarina Hari Za Su Dandana Kudarsu - Tambuwal

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari

Za A Dinga Tunawa Da Buhari A Matsayin Waliyyi A Siyasar Nijeriya —Dakta Zangina

July 18, 2025
Hanya Mai Salon Musamman Da Kasar Sin Take Bi Wajen Raya Harkokin Kudi

Hanya Mai Salon Musamman Da Kasar Sin Take Bi Wajen Raya Harkokin Kudi

July 18, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Tinubu Ya Nada Ɗan Babangida A Matsayin Shugaban Bankin Manoma

July 18, 2025
‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas

‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas

July 18, 2025
Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba

Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba

July 18, 2025
Al’umma Na Kokawa Kan Tsadar Kayan Miya A Sassan Kasar Nan

Al’umma Na Kokawa Kan Tsadar Kayan Miya A Sassan Kasar Nan

July 18, 2025
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dillalai Sun Rage Farashin Man Fetur A Nijeriya

July 18, 2025
Ko Kaɗan Bamu Ji Takaicin Ficewar Atiku Daga Jam’iyyar PDP Ba — Damagum

Ko Kaɗan Bamu Ji Takaicin Ficewar Atiku Daga Jam’iyyar PDP Ba — Damagum

July 18, 2025
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

Akwai Bukatar Daina Cin Zarafin Malaman Makaranta

July 18, 2025
Nazari Game Da Rayuwar Muhammadu Buhari

Nazari Game Da Rayuwar Muhammadu Buhari

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.