• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ne Kadai Zai Iya Magance Rashin Tsaro Da Tabarbarewar Tattalin Arziki – Buhari 

by Sadiq
3 years ago
Tinubu

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya bukaci masu kada kuri’a a Jihar Yobe da kuma yankin Arewa Maso Gabashin kasar nan da su tabbatar da cewa sun zabi Bola Ahmed Tinubu a zabe mai zuwa.

Da yake jawabi a taron yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC a filin wasa na Damaturu, babban birnin Jihar Yobe, shugaban kasar a wata sanarwa ta hannun mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Femi Adesina, ya ce zaben Tinubu da abokin takararsa, Kashim Shettima, ne kadai mafitar ‘yan Nijeriya.

  • Birtaniya Na Son Taimaka Wa Nijeriya Ta Farfado – Atiku 
  • Aikin Hajjin 2023: Nijeriya Ta Kulla Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Gwamnatin Saudiyya

Ya ce idan ana bukatar tabbatar da dorewar ci gaban da aka samu a fannin tsaro, tattalin arziki da ilimi a kasar nan dole a zabi dan takarar na APC.

Shugaban ya sha alwashin cewa bayan nasarar da aka samu a kan ‘yan ta’adda a yankin, gwamnatin APC ta yi kokarin karya lagon duk wanda ke barazana ga hadin kan Nijeriya.

Shugaban da yake jaddada bukatar ilimi wajen yakar akidar ta’addanci ta Boko Haram, ya shaida wa iyaye a Yobe cewa: “Ku tabbata kun tura ‘ya’yanku makaranta ku fahimtar da su cewa duk abin da kuke da shi a duniya za a iya kwace muku, ilimi ne kadai ba za a iya kwace muku ba.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

‘‘Ni maraya ne; ban san mahaifina ba. Na yi shekara tara a makarantar kwana kuma saboda ilimi aka kai ni aikin sojin Nijeriya.”

Ga masu rike da tutar jam’iyyar APC a zabe mai zuwa, shugaba Buhari ya kalubalanci su da su tabbatar da shugabanci na gari idan aka zabe su, ka da su bai wa jama’a kunya.

Ya bayyana cewa jam’iyyar mai mulki ta yi iya bakin kokarinta a cikin shekaru takwas da suka gabata a matakin tarayya kuma za ta ci gaba da tabbatar da ci gaba, wadata da kwanciyar hankali a Nijeriya.

A nasa jawabin, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya bukaci ‘yan Nijeriya da su yi watsi da karairayi da jam’iyyun adawa ke yi wa gwamnatin Buhari.

“Wannan gwamnati gwamnati ce ta ci gaba, rikon amana da gaskiya,” in ji shi.

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, wanda ya yaba wa Buhari kan samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin Arewa maso Gabashin kasar nan, ya yi alkawarin cewa gwamnatinsa za ta mayar da yankin cibiyar sarrafa kayan gona ta Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai
Manyan Labarai

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

October 30, 2025
Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

October 30, 2025
Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar
Manyan Labarai

Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

October 30, 2025
Next Post
Dan Takarar Gwamnan PDP Ya Nemi Goyon Bayan Ma’aikata A Kaduna

Dan Takarar Gwamnan PDP Ya Nemi Goyon Bayan Ma'aikata A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

October 30, 2025
Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

October 30, 2025
Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

October 30, 2025
Tinubu Ya Nada Musa Aliyu A Matsayin Shugaban ICPC

Tinubu Ya Amince Da Ƙara Harajin Shigo Da Man Fetur Da Dizal Zuwa Kashi 15

October 30, 2025
Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

October 30, 2025
Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

October 30, 2025
Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

October 30, 2025
Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

October 30, 2025
Tinubu

Bai Kamata Gwamnati Ta Ke Ciyo Bashi Bayan Cire Tallafin Man Fetur Ba – Sanusi II

October 30, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Sauya Sunayen Waɗanda Aka Yi Wa Afuwa

October 30, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.