• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bashin Naira Biliyan 2.5: Duhu Ya Mamaye Ma’aikatun Sakkwato Da Zamfara

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
3 years ago
Zamfara

Ma’aikatu da Hukumomin Gwamnatocin Jihohin Sakkwato da Zamfara sun kasance a cikin duhu bakidaya a yayin da Hukumar Wutar Lantarki ta Kaduna (KEDCO) ta tsinke layukan wutar a dalilin dimbin bashi.

Kamfanin KEDCO ya bayyana cewar ba ya da wani zabi face daukar matakin yanke wutar bayan cikar wa’adin makwanni uku da suka baiwa Gwamnatocin domin su biya tarin bashin da kamfanin ke bin su ko su saka su a duhu.

  • Gina Al‘ummar Sin Da Afirka Mai Koshin Lafiya Ba Batu Ne Na Fatar Baki Ba 
  • An Raba Wa Jami’an Tsaro Na NSCDC 7 Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe Cakin Banki Da Guraben Aiki

Shugaban sashen Yada Labarai na KEDCO Abdul’aziz Abdallah a sanarwar da ya fitar makon jiya ya bayyana cewar kamfanin na bin Gwamnatin Jihar Sakkwato tsabar kudi naira biliyan 1, 496, 313, 156 a yayin da Gwamnatin Zamfara ke rike da bashin kamfanin na naira biliyan 1, 040, 506, 740 daga watan Disamba 2022.

Yanke layukan ya haifar da tarin illoli da dama a Ma’aikatu da Hukumomin Gwamnatocin biyu kasancewar ayyukan yau da kullum na gudanar da ofisoshi da dama sun tsaya, wasu kuma ba su tafiya yadda ya kamata.

A wasu ma’aikatu ba su da zabi face amfani da injinin janareta domin haskaka ma’aikatun da kuma aiwatar da ayyukan da suka wajaba a gare su.

LABARAI MASU NASABA

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Sanarwar ta bayyana cewar yanke wutar shine mataki na karshe da za su iya dauka musamman saboda rashin biyan bashin wanda KEDCO ta bayyana cewar ba wai hakan na kawo masu cikas wajen aiwatar da ayyukan su ne kawai ba, yana kuma zamar masu matukar wahala wajen sauke nauyin da ke kan su na baiwa al’umma haske da kuma samun ribar da za su kara inganta ayyukan su.

“Abin damuwa ne yadda Gwamnatin Zamfara ta kasa biyan kudin wuta a tsawon watanni 12 da suka gabata a yayin da Jihar Sakkwato ta kasa biyan wuta na tsawon watanni hudu.”

Bayanin ya nuna cewar Hukumar KEDCO ta dauki matakin bayar sanar da Gwamnatocin bukatar biyan basukan da kuma notis na karshe bayan da dukkanin alkawulan da suka dauka na biyan kudaden ya faskara duk da an yi ta tunatarwa.

Kamfanin na KEDCO ya bayyana cewar ya wajaba ga kamfanin su rika biyan kashi 100 na wutar da suke karba da na gudanarwa wanda akwai hukunci idan suka saba wanda a kan hakan kamfanin ya ce wannan dalilin ne ya sa suke fadi tashi a kowane wata amma abin kan faskara saboda karanci, rashin biya da biyan wuta ba bisa ka’ida ba.

“Muna bayar da tabbacin cewar a shirye muke mu mayar da hasken wuta a ma’aikatun Gwamnatocin biyu da muka yanke idan aka dauki matakan da ya kamata na biyan dadadden bashin da kuma tabbacin ci-gaba da biyan wuta yadda ya kamata a cikin lokaci.” In ji kamfanin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 
Manyan Labarai

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya
Manyan Labarai

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro
Manyan Labarai

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025
Next Post
Masarautar Katsina Ta Warware Rawanin Hakimin Bakori, Makaman Katsina

Masarautar Katsina Ta Warware Rawanin Hakimin Bakori, Makaman Katsina

LABARAI MASU NASABA

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

November 3, 2025
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.