• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bashin Naira Biliyan 2.5: Duhu Ya Mamaye Ma’aikatun Sakkwato Da Zamfara

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Bashin Naira Biliyan 2.5: Duhu Ya Mamaye Ma’aikatun Sakkwato Da Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ma’aikatu da Hukumomin Gwamnatocin Jihohin Sakkwato da Zamfara sun kasance a cikin duhu bakidaya a yayin da Hukumar Wutar Lantarki ta Kaduna (KEDCO) ta tsinke layukan wutar a dalilin dimbin bashi.

Kamfanin KEDCO ya bayyana cewar ba ya da wani zabi face daukar matakin yanke wutar bayan cikar wa’adin makwanni uku da suka baiwa Gwamnatocin domin su biya tarin bashin da kamfanin ke bin su ko su saka su a duhu.

  • Gina Al‘ummar Sin Da Afirka Mai Koshin Lafiya Ba Batu Ne Na Fatar Baki Ba 
  • An Raba Wa Jami’an Tsaro Na NSCDC 7 Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe Cakin Banki Da Guraben Aiki

Shugaban sashen Yada Labarai na KEDCO Abdul’aziz Abdallah a sanarwar da ya fitar makon jiya ya bayyana cewar kamfanin na bin Gwamnatin Jihar Sakkwato tsabar kudi naira biliyan 1, 496, 313, 156 a yayin da Gwamnatin Zamfara ke rike da bashin kamfanin na naira biliyan 1, 040, 506, 740 daga watan Disamba 2022.

Yanke layukan ya haifar da tarin illoli da dama a Ma’aikatu da Hukumomin Gwamnatocin biyu kasancewar ayyukan yau da kullum na gudanar da ofisoshi da dama sun tsaya, wasu kuma ba su tafiya yadda ya kamata.

A wasu ma’aikatu ba su da zabi face amfani da injinin janareta domin haskaka ma’aikatun da kuma aiwatar da ayyukan da suka wajaba a gare su.

Labarai Masu Nasaba

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sanarwar ta bayyana cewar yanke wutar shine mataki na karshe da za su iya dauka musamman saboda rashin biyan bashin wanda KEDCO ta bayyana cewar ba wai hakan na kawo masu cikas wajen aiwatar da ayyukan su ne kawai ba, yana kuma zamar masu matukar wahala wajen sauke nauyin da ke kan su na baiwa al’umma haske da kuma samun ribar da za su kara inganta ayyukan su.

“Abin damuwa ne yadda Gwamnatin Zamfara ta kasa biyan kudin wuta a tsawon watanni 12 da suka gabata a yayin da Jihar Sakkwato ta kasa biyan wuta na tsawon watanni hudu.”

Bayanin ya nuna cewar Hukumar KEDCO ta dauki matakin bayar sanar da Gwamnatocin bukatar biyan basukan da kuma notis na karshe bayan da dukkanin alkawulan da suka dauka na biyan kudaden ya faskara duk da an yi ta tunatarwa.

Kamfanin na KEDCO ya bayyana cewar ya wajaba ga kamfanin su rika biyan kashi 100 na wutar da suke karba da na gudanarwa wanda akwai hukunci idan suka saba wanda a kan hakan kamfanin ya ce wannan dalilin ne ya sa suke fadi tashi a kowane wata amma abin kan faskara saboda karanci, rashin biya da biyan wuta ba bisa ka’ida ba.

“Muna bayar da tabbacin cewar a shirye muke mu mayar da hasken wuta a ma’aikatun Gwamnatocin biyu da muka yanke idan aka dauki matakan da ya kamata na biyan dadadden bashin da kuma tabbacin ci-gaba da biyan wuta yadda ya kamata a cikin lokaci.” In ji kamfanin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BashiZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Bauchi Ta Fayyace Zare Da Abawa Kan Filin Makabarta A Yolan Bayara

Next Post

Masarautar Katsina Ta Warware Rawanin Hakimin Bakori, Makaman Katsina

Related

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

4 hours ago
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

8 hours ago
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa
Manyan Labarai

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

8 hours ago
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

9 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

12 hours ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

1 day ago
Next Post
Masarautar Katsina Ta Warware Rawanin Hakimin Bakori, Makaman Katsina

Masarautar Katsina Ta Warware Rawanin Hakimin Bakori, Makaman Katsina

LABARAI MASU NASABA

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.