ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bashin Naira Biliyan 2.5: Duhu Ya Mamaye Ma’aikatun Sakkwato Da Zamfara

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
3 years ago
Zamfara

Ma’aikatu da Hukumomin Gwamnatocin Jihohin Sakkwato da Zamfara sun kasance a cikin duhu bakidaya a yayin da Hukumar Wutar Lantarki ta Kaduna (KEDCO) ta tsinke layukan wutar a dalilin dimbin bashi.

Kamfanin KEDCO ya bayyana cewar ba ya da wani zabi face daukar matakin yanke wutar bayan cikar wa’adin makwanni uku da suka baiwa Gwamnatocin domin su biya tarin bashin da kamfanin ke bin su ko su saka su a duhu.

  • Gina Al‘ummar Sin Da Afirka Mai Koshin Lafiya Ba Batu Ne Na Fatar Baki Ba 
  • An Raba Wa Jami’an Tsaro Na NSCDC 7 Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe Cakin Banki Da Guraben Aiki

Shugaban sashen Yada Labarai na KEDCO Abdul’aziz Abdallah a sanarwar da ya fitar makon jiya ya bayyana cewar kamfanin na bin Gwamnatin Jihar Sakkwato tsabar kudi naira biliyan 1, 496, 313, 156 a yayin da Gwamnatin Zamfara ke rike da bashin kamfanin na naira biliyan 1, 040, 506, 740 daga watan Disamba 2022.

ADVERTISEMENT

Yanke layukan ya haifar da tarin illoli da dama a Ma’aikatu da Hukumomin Gwamnatocin biyu kasancewar ayyukan yau da kullum na gudanar da ofisoshi da dama sun tsaya, wasu kuma ba su tafiya yadda ya kamata.

A wasu ma’aikatu ba su da zabi face amfani da injinin janareta domin haskaka ma’aikatun da kuma aiwatar da ayyukan da suka wajaba a gare su.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Sanarwar ta bayyana cewar yanke wutar shine mataki na karshe da za su iya dauka musamman saboda rashin biyan bashin wanda KEDCO ta bayyana cewar ba wai hakan na kawo masu cikas wajen aiwatar da ayyukan su ne kawai ba, yana kuma zamar masu matukar wahala wajen sauke nauyin da ke kan su na baiwa al’umma haske da kuma samun ribar da za su kara inganta ayyukan su.

“Abin damuwa ne yadda Gwamnatin Zamfara ta kasa biyan kudin wuta a tsawon watanni 12 da suka gabata a yayin da Jihar Sakkwato ta kasa biyan wuta na tsawon watanni hudu.”

Bayanin ya nuna cewar Hukumar KEDCO ta dauki matakin bayar sanar da Gwamnatocin bukatar biyan basukan da kuma notis na karshe bayan da dukkanin alkawulan da suka dauka na biyan kudaden ya faskara duk da an yi ta tunatarwa.

Kamfanin na KEDCO ya bayyana cewar ya wajaba ga kamfanin su rika biyan kashi 100 na wutar da suke karba da na gudanarwa wanda akwai hukunci idan suka saba wanda a kan hakan kamfanin ya ce wannan dalilin ne ya sa suke fadi tashi a kowane wata amma abin kan faskara saboda karanci, rashin biya da biyan wuta ba bisa ka’ida ba.

“Muna bayar da tabbacin cewar a shirye muke mu mayar da hasken wuta a ma’aikatun Gwamnatocin biyu da muka yanke idan aka dauki matakan da ya kamata na biyan dadadden bashin da kuma tabbacin ci-gaba da biyan wuta yadda ya kamata a cikin lokaci.” In ji kamfanin.

Zamfara
Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
+ postsBio
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    A Yayin Da Babban Bankin Ƙasa (CBN) Ke Yaƙi Da Laifukan Intanet
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Halin Da Matsalar Tsaro Ta Jefa ‘Yan Gudun Hijira A Arerwacin Nijeriya
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Sanata Tambuwal Ya Sadaukar Da Takararsa Ga Faruku Yabo
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Dan-Iya Ya Zama Ɗan Takarar Gwamnan ADC A Sakkwato

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Masarautar Katsina Ta Warware Rawanin Hakimin Bakori, Makaman Katsina

Masarautar Katsina Ta Warware Rawanin Hakimin Bakori, Makaman Katsina

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.