• English
  • Business News
Friday, August 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Tabbatar Da Nasarar Tsarin Ba Da Inshorar Kiwon Lafiya A Kebbi – Dakta Augie

by Umar Faruk
3 years ago
in Labarai
0
Za Mu Tabbatar Da Nasarar Tsarin Ba Da Inshorar Kiwon Lafiya A Kebbi – Dakta Augie
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar kula da Inshorar kiwon lafiya ta jihar Kebbi (KECHEMA) ta dorawa kungiyoyin farar hula, kungiyoyin kwadago, kwararrun ma’aikatan lafiya da kuma kafafen yada labarai aikin bayar da shawarwari da yada labarai ga jama’a kan shirin Inshorar kiwon lafiya na hukumar a jihar.

 

Sakataren zartarwa na hukumar Dakta Jafar Augie ne ya bukaci hakan a wajen bikin rufe taron na kwanaki biyu da aka gudanar a Sukura Otal da ke jihar Sakkwato wanda aka shirya tare da hadin gwiwar hukumar lafiya ta Integrated Health Programme (IHP).

  • Buhari Ya Yi Jajen Hatsarin Jirgin Ruwa A Kebbi

Ya ce, “Shirin na mu ne a matsayinmu na ’yan uwa da masu ruwa da tsaki a lokaci guda; ba na gwamnati ba ne, don haka ya rage gare mu na tabbatar da tsarin ya samun nasara ko akasin haka,’ Inji shi.

 

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi

Cire Tallafin Mai Ya Taimaka Mana Wajen Aiwatar da Ayyuka, In Ji Gwamna Mbah

“Ya kamata mu rungumi tsarin mu mallake shi kamar yadda gwamnati ta yi aikinta ta hanyar ba wa tsarin doka da ka’idojin gudanar da aiki da kuma wuraren da suka dace.

 

“Babu abinci kyauta yanzu a duniya; dole ne mu ba da gudummawa don haɓaka ingantaccen isar da lafiya. Allah zai iya kalubalance mu idan muka zabi rashin tausayin jama’amu ga kula da kiwon lafiya,” inji shi.

 

Augie ya bukaci masu ruwa da tsaki da su tabbatar da dorewar da kuma tsayuwar tsarin Inshorar kiwon lafiya wajen samar da kudaden da za su bayar da gudummuwar cin nasarar tsarin, yana mai cewa alhakin ya rataya ne a kan dukkan masu ruwa da tsaki.

 

A cewarsa, hukumar na da hurumin tabbatar da ingantacciyar hidimar kiwon lafiya ga kowa da kowa a jihar.

 

Haka zalika Dokta Augie ya yaba wa mahalarta taron, wadanda ya bayyana a matsayin, dukkan muhimman membobi na kungiyar aiki na fasaha kuma sun ba da himma wajen tsara tsarin.

 

“Za mu ci gaba da kasancewa masu godiya. Muna matukar godiya ga abokan aikinmu na ci gaba, USAID da hukumominta masu ba da tallafi ga kiwon lafiya da gudanar da mulki da Integrated Health Project (IHP) da sauransu,” in ji sakataren.

 

A nata bangaren, mai ba da shawara kan harkokin kudade da kasafi na IHP, Dakta Aisha Aminu-Senchi, ta bayyana cewa, IHP na hada kai da gwamnatocin jihohi wajen karfafawa da kuma ciyar da ayyukan inshorar lafiya na jihohi gaba, domin cimma burin samar da kiwon lafiya na duniya baki daya.

 

Ta bayyana cewa talakawan kasa ba za su iya biyan kudaden da samar da Inshorar lafiyar kansu ba, tana mai cewa ya kamata ’yan kasa masu wadata da su rika biyama wadanda ba su don amfani da kuma masu karamin karfi don iya dogaro da kai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sinawa ‘Yan Sama Jannati Sun Gabatar Da Gaisuwar Sabuwar Shekara Daga Cibiyar Binciken Sararin Samaniya

Next Post

Gwamnan Gombe Ya Bada Tallafin Miliyan 25 Ga Ƙungiyar CAN Don Gina Masaukin Baki

Related

Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi

2 hours ago
Cire Tallafin Mai Ya Taimaka Mana Wajen Aiwatar da Ayyuka, In Ji Gwamna Mbah
Labarai

Cire Tallafin Mai Ya Taimaka Mana Wajen Aiwatar da Ayyuka, In Ji Gwamna Mbah

3 hours ago
An Taƙaita Zirga-Zirga A Ƙananan Hukumomi 4 Kafin Zaben Cike Gurbi A Kano
Labarai

An Taƙaita Zirga-Zirga A Ƙananan Hukumomi 4 Kafin Zaben Cike Gurbi A Kano

3 hours ago
Shugaba Tinubu Ya Naɗa Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Naɗa Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci

5 hours ago
Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda
Rahotonni

Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda

5 hours ago
Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa
Manyan Labarai

Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa

6 hours ago
Next Post
Gwamnan Gombe Ya Bada Tallafin Miliyan 25 Ga Ƙungiyar CAN Don Gina Masaukin Baki

Gwamnan Gombe Ya Bada Tallafin Miliyan 25 Ga Ƙungiyar CAN Don Gina Masaukin Baki

LABARAI MASU NASABA

GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

August 15, 2025
Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama

Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama

August 15, 2025
Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi

Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi

August 15, 2025
Cire Tallafin Mai Ya Taimaka Mana Wajen Aiwatar da Ayyuka, In Ji Gwamna Mbah

Cire Tallafin Mai Ya Taimaka Mana Wajen Aiwatar da Ayyuka, In Ji Gwamna Mbah

August 15, 2025
NPA Ta Fito Da Sabuwar Doka Kan Kayan Da Ake Ajiyewa A Tashoshinta

NPA Ta Fito Da Sabuwar Doka Kan Kayan Da Ake Ajiyewa A Tashoshinta

August 15, 2025
An Taƙaita Zirga-Zirga A Ƙananan Hukumomi 4 Kafin Zaben Cike Gurbi A Kano

An Taƙaita Zirga-Zirga A Ƙananan Hukumomi 4 Kafin Zaben Cike Gurbi A Kano

August 15, 2025
Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata

Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata

August 15, 2025
Shugaba Tinubu Ya Naɗa Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci

Shugaba Tinubu Ya Naɗa Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci

August 15, 2025
Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda

Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda

August 15, 2025
Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa

Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa

August 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.