ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Gombe Ya Bada Tallafin Miliyan 25 Ga Ƙungiyar CAN Don Gina Masaukin Baki

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Gwamnan Gombe

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bai wa kungiyar Kiristoci ta kasa a jihar (CAN) tallafin naira miliyan 25 domin gina masaukin baki na kungiyar tare da karin wasu naira miliyan 15 don shingace cibiyar da sauran ayyuka.

 

Tallafin kudin na zuwa ne a lokacin da mambobin Ƙungiyar Kiristoci a Jihar Gombe suka kai wa gwamnan ziyarar bangirma ta sabuwar shekara.

ADVERTISEMENT
  • 2023: Mai Binciken Kudin PDP Da Wasu Jiga-jigan Jam’iyyar Sun Koma NNPP A Gombe

Shugaban Kungiyar Kiristoci ta Nijeriya, CAN reshen Jihar Gombe, Rev. Fr. Joseph Alphonsus Shinga yayin ziyarar ya ce mabiya Addinin Kirista a jihar su na alfahari da irin ayyukan da Gwamnan yake yi a fannin samar da ababen more rayuwa a sassa masu muhimmanci na tattalin arzikin jihar, yana mai jaddada cewa idan ya sake samun dama a karo na biyu, jihar za ta shiga wani sabon salo na ci gaba da wadata.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Shinga ya kuma yaba da irin goyon bayan da Gwamna ke bai wa kungiyar CAN, yana mai cewa gwamnan yana bin Kiristocin jihar bashi na ci gaba da goyon bayan manufofi da shirye-shiryen gwamnatin sa, saboda halayen sa ababen koyi.

 

Ya godewa Gwamnan bisa daukar nauyin Kiristoci 33 da suka yi aikin ibada a kasar Isra’ila da Jordan a 2022, ya kuma buƙaci a ci gaba da wannan tallafi.

 

Sai ya yi kira ga Gwamna Inuwa Yahaya, ya taimakawa kungiyar wajen samar da ruwan sha ga cibiyar ta CAN, ya kuma bukaci tallafin kudi don gina masaukin baki na kungiyar wanda gwamnatinsa ta taimaka wajen ginata ta hanyar tallafin daya bayar a baya.

 

A nasa jawabin, Gwamna Inuwa ya godewa al’ummar Kiristocin jihar bisa hadin kan da suke bai wa jihar wajen wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali, musamman idan aka kwatanta da kalubalen tsaron da jihohin dake shiyyar Arewa maso Gabas ke fuskanta da sauran su.

 

Ya ce saboda zaman lafiya da kwanciyar hankalin da ake samu a jihar ya sa gwamnatinsa ke iya gudanar da ayyuka don tabbatar da ci gaban al’umma da bunkasa tattalin arziki da ababen more rayuwa, don haka ya bukaci al’ummar jihar su zamto masu kishi da kiyaye duk wani abu da zai kawo cikas ga zaman lafiya.

 

Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana cewa, a yayin bikin Kirsimeti, gwamnatin sa ta bada tallafin kuɗi fiye da Naira miliyan 90 domin tallafawa al’ummar Kirista a jihar wajen gudanar da bukukuwan su cikin sauƙi duba da halin da tattalin arziƙin ƙasar ke ciki.

 

Ya kuma sanar da kyautar Naira miliyan 10 ga Kiristocin a matsayin goron sabuwar shekara, inda aka ware Naira miliyan 5 ga mata da kuma wasu miliyan biyar ga maza.

 

“Hakazalika dangane da bukatar ku ta tallafi a harkar samar da ruwan sha a cibiyar ta CAN, kamar yadda kuka sani muna kan aikin fadada shirin samar da ruwan sha na Gombe, kuma na yi imanin cewa kwanan nan kun ga Ministan Albarkatun Ruwa ya zo ya kaddamar da aikin inda gwamnati ke kashe fiye da Naira biliyan 11.68 don samar da ruwan sha ga al’ummar da aka yi watsi da ita, musamman ma yankunan Tunfure har zuwa cibiyar taro ta ƙasa da ƙasa da kewaye”.

 

Gwamna Inuwa Yahaya ya yi amfani da damar wajen yin kira ga al’ummar jihar su karbi katin zaben na dindindin don yun amfani da ‘yancin su su zabi ‘yan takaran da suke so.

Gwamnan Gombe
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
2023: Ina Neman Tazarce Ne Domin Cigaba Da Shimfida Ayyukan Raya Bauchi – Gwamna Bala

2023: Ina Neman Tazarce Ne Domin Cigaba Da Shimfida Ayyukan Raya Bauchi - Gwamna Bala

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.