ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Tabbatar Da Nasarar Tsarin Ba Da Inshorar Kiwon Lafiya A Kebbi – Dakta Augie

by Umar Faruk
3 years ago
Augie

Hukumar kula da Inshorar kiwon lafiya ta jihar Kebbi (KECHEMA) ta dorawa kungiyoyin farar hula, kungiyoyin kwadago, kwararrun ma’aikatan lafiya da kuma kafafen yada labarai aikin bayar da shawarwari da yada labarai ga jama’a kan shirin Inshorar kiwon lafiya na hukumar a jihar.

 

Sakataren zartarwa na hukumar Dakta Jafar Augie ne ya bukaci hakan a wajen bikin rufe taron na kwanaki biyu da aka gudanar a Sukura Otal da ke jihar Sakkwato wanda aka shirya tare da hadin gwiwar hukumar lafiya ta Integrated Health Programme (IHP).

ADVERTISEMENT
  • Buhari Ya Yi Jajen Hatsarin Jirgin Ruwa A Kebbi

Ya ce, “Shirin na mu ne a matsayinmu na ’yan uwa da masu ruwa da tsaki a lokaci guda; ba na gwamnati ba ne, don haka ya rage gare mu na tabbatar da tsarin ya samun nasara ko akasin haka,’ Inji shi.

 

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

“Ya kamata mu rungumi tsarin mu mallake shi kamar yadda gwamnati ta yi aikinta ta hanyar ba wa tsarin doka da ka’idojin gudanar da aiki da kuma wuraren da suka dace.

 

“Babu abinci kyauta yanzu a duniya; dole ne mu ba da gudummawa don haɓaka ingantaccen isar da lafiya. Allah zai iya kalubalance mu idan muka zabi rashin tausayin jama’amu ga kula da kiwon lafiya,” inji shi.

 

Augie ya bukaci masu ruwa da tsaki da su tabbatar da dorewar da kuma tsayuwar tsarin Inshorar kiwon lafiya wajen samar da kudaden da za su bayar da gudummuwar cin nasarar tsarin, yana mai cewa alhakin ya rataya ne a kan dukkan masu ruwa da tsaki.

 

A cewarsa, hukumar na da hurumin tabbatar da ingantacciyar hidimar kiwon lafiya ga kowa da kowa a jihar.

 

Haka zalika Dokta Augie ya yaba wa mahalarta taron, wadanda ya bayyana a matsayin, dukkan muhimman membobi na kungiyar aiki na fasaha kuma sun ba da himma wajen tsara tsarin.

 

“Za mu ci gaba da kasancewa masu godiya. Muna matukar godiya ga abokan aikinmu na ci gaba, USAID da hukumominta masu ba da tallafi ga kiwon lafiya da gudanar da mulki da Integrated Health Project (IHP) da sauransu,” in ji sakataren.

 

A nata bangaren, mai ba da shawara kan harkokin kudade da kasafi na IHP, Dakta Aisha Aminu-Senchi, ta bayyana cewa, IHP na hada kai da gwamnatocin jihohi wajen karfafawa da kuma ciyar da ayyukan inshorar lafiya na jihohi gaba, domin cimma burin samar da kiwon lafiya na duniya baki daya.

 

Ta bayyana cewa talakawan kasa ba za su iya biyan kudaden da samar da Inshorar lafiyar kansu ba, tana mai cewa ya kamata ’yan kasa masu wadata da su rika biyama wadanda ba su don amfani da kuma masu karamin karfi don iya dogaro da kai.

Augie
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Sace ‘Yan Makarantar Mata Ta Kebbi: Abubuwan Da Ba A Fada Ba
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Naɗa Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru 

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Gwamnan Gombe Ya Bada Tallafin Miliyan 25 Ga Ƙungiyar CAN Don Gina Masaukin Baki

Gwamnan Gombe Ya Bada Tallafin Miliyan 25 Ga Ƙungiyar CAN Don Gina Masaukin Baki

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.