• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Gombe Ya Bada Tallafin Miliyan 25 Ga Ƙungiyar CAN Don Gina Masaukin Baki

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnan Gombe Ya Bada Tallafin Miliyan 25 Ga Ƙungiyar CAN Don Gina Masaukin Baki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bai wa kungiyar Kiristoci ta kasa a jihar (CAN) tallafin naira miliyan 25 domin gina masaukin baki na kungiyar tare da karin wasu naira miliyan 15 don shingace cibiyar da sauran ayyuka.

 

Tallafin kudin na zuwa ne a lokacin da mambobin Ƙungiyar Kiristoci a Jihar Gombe suka kai wa gwamnan ziyarar bangirma ta sabuwar shekara.

  • 2023: Mai Binciken Kudin PDP Da Wasu Jiga-jigan Jam’iyyar Sun Koma NNPP A Gombe

Shugaban Kungiyar Kiristoci ta Nijeriya, CAN reshen Jihar Gombe, Rev. Fr. Joseph Alphonsus Shinga yayin ziyarar ya ce mabiya Addinin Kirista a jihar su na alfahari da irin ayyukan da Gwamnan yake yi a fannin samar da ababen more rayuwa a sassa masu muhimmanci na tattalin arzikin jihar, yana mai jaddada cewa idan ya sake samun dama a karo na biyu, jihar za ta shiga wani sabon salo na ci gaba da wadata.

 

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Shinga ya kuma yaba da irin goyon bayan da Gwamna ke bai wa kungiyar CAN, yana mai cewa gwamnan yana bin Kiristocin jihar bashi na ci gaba da goyon bayan manufofi da shirye-shiryen gwamnatin sa, saboda halayen sa ababen koyi.

 

Ya godewa Gwamnan bisa daukar nauyin Kiristoci 33 da suka yi aikin ibada a kasar Isra’ila da Jordan a 2022, ya kuma buƙaci a ci gaba da wannan tallafi.

 

Sai ya yi kira ga Gwamna Inuwa Yahaya, ya taimakawa kungiyar wajen samar da ruwan sha ga cibiyar ta CAN, ya kuma bukaci tallafin kudi don gina masaukin baki na kungiyar wanda gwamnatinsa ta taimaka wajen ginata ta hanyar tallafin daya bayar a baya.

 

A nasa jawabin, Gwamna Inuwa ya godewa al’ummar Kiristocin jihar bisa hadin kan da suke bai wa jihar wajen wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali, musamman idan aka kwatanta da kalubalen tsaron da jihohin dake shiyyar Arewa maso Gabas ke fuskanta da sauran su.

 

Ya ce saboda zaman lafiya da kwanciyar hankalin da ake samu a jihar ya sa gwamnatinsa ke iya gudanar da ayyuka don tabbatar da ci gaban al’umma da bunkasa tattalin arziki da ababen more rayuwa, don haka ya bukaci al’ummar jihar su zamto masu kishi da kiyaye duk wani abu da zai kawo cikas ga zaman lafiya.

 

Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana cewa, a yayin bikin Kirsimeti, gwamnatin sa ta bada tallafin kuɗi fiye da Naira miliyan 90 domin tallafawa al’ummar Kirista a jihar wajen gudanar da bukukuwan su cikin sauƙi duba da halin da tattalin arziƙin ƙasar ke ciki.

 

Ya kuma sanar da kyautar Naira miliyan 10 ga Kiristocin a matsayin goron sabuwar shekara, inda aka ware Naira miliyan 5 ga mata da kuma wasu miliyan biyar ga maza.

 

“Hakazalika dangane da bukatar ku ta tallafi a harkar samar da ruwan sha a cibiyar ta CAN, kamar yadda kuka sani muna kan aikin fadada shirin samar da ruwan sha na Gombe, kuma na yi imanin cewa kwanan nan kun ga Ministan Albarkatun Ruwa ya zo ya kaddamar da aikin inda gwamnati ke kashe fiye da Naira biliyan 11.68 don samar da ruwan sha ga al’ummar da aka yi watsi da ita, musamman ma yankunan Tunfure har zuwa cibiyar taro ta ƙasa da ƙasa da kewaye”.

 

Gwamna Inuwa Yahaya ya yi amfani da damar wajen yin kira ga al’ummar jihar su karbi katin zaben na dindindin don yun amfani da ‘yancin su su zabi ‘yan takaran da suke so.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Za Mu Tabbatar Da Nasarar Tsarin Ba Da Inshorar Kiwon Lafiya A Kebbi – Dakta Augie

Next Post

2023: Ina Neman Tazarce Ne Domin Cigaba Da Shimfida Ayyukan Raya Bauchi – Gwamna Bala

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

8 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

10 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

11 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

15 hours ago
Gwamnan Gombe
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

16 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

17 hours ago
Next Post
2023: Ina Neman Tazarce Ne Domin Cigaba Da Shimfida Ayyukan Raya Bauchi – Gwamna Bala

2023: Ina Neman Tazarce Ne Domin Cigaba Da Shimfida Ayyukan Raya Bauchi - Gwamna Bala

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.