• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Kabilanci: An Gudanar Da Taron Yafe Wa Juna A Jihar Filato

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Rikicin Kabilanci: An Gudanar Da Taron Yafe Wa Juna A Jihar Filato
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Filato ta jagoranci wani gagarumin taro a birnin Jos domin yafe wa juna da kuma sasanta al’ummar jihar da rikicin kabilanci da Addini ya raba kawunansu.

Wannan biki ya gudana ne a karkashin jagorancin gwamnan jihar, Simon Bako Lalong wanda ya samu halartar Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar II da Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero da shugaban mabiya darikar Katolika na Nijeriya, Arch Bishop John Onayekan da ya samu wakilcin Arch Bishop Ignatius Kaigama.

  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Kai Zuciya Nesa Game Da Batun Kumbon Farar Hula Da Ta Harbo
  • Zan Tabbatar Da An Ci Gajiyar Man Fetur A Yankin Bauchi Da Gombe Muddin Aka Zabe Ni – Atiku

Yayin gudanar da jawabinsa, gwamna Lalong wanda ya bayyana farin cikinsa da yadda jama’a suka amsa kiran da ya musu, ya ce sun yi nasarar kafa ginshikin zaman lafiya da adalci da mutunta juna da kuma karbar baki.

Lalong, ya ce da taimakon sarakunan gargajiya da limaman Addinai da shugabannin al’umma, gwamnatinsa ta yi aiki tukuru wajen sake fasalin jihar da kuma hada kan jama’a.

Gwamnan, ya ce kokarin da suka yi, ya taimaka wajen kawar da tsoro da rashin amincewa juna da kuma kyamar da ake samu a tsakanin jama’ar jihar da suka fito daga kabilu daban-daban

Labarai Masu Nasaba

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Lalong ya bukaci jama’ar Jihar Filato da su rungumi shirin yafe wa juna da kuma hadin kai, yayin da shi ma ya nemi gafarar jama’ar da suke zaton ya saba musu.

Yayin jawabinsa, Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Saad Abubakar, ya jinjina wa gwamnatin Jihar Filato saboda jajircewar da ta yi wajen ganin ta tabbatar da dorewar zaman lafiya, musamman ganin yadda zaman lafiya da walwala ke dawowa a tsakanin al’umma.

Sarkin Musulmin ya ce babu dalilin da zai sa bayan an kwashe shekaru aru-aru ana zaman lafiya a Jihar, a ce kuma yanzu wasu ‘yan tsiraru za su hana zaman lafiya, yayin da ya gargadi jama’a da su daina barin bata gari suna tunzira su domin tashin hankali ba.

A nashi jawabin, Arch Bishop Ignatius Kaigama, shugaban mabiya darikar Katolika ya bayyana farin cikinsa cewar kokarin da suka yi a Filato na tabbatar da zaman lafiya ya kankama, sakamakon rawar da gwamnatin jihar ta taka.

Shugaban sarakunan Jihar Filato, Gbong Gwom Jos, Jacob Gyang Buba, ya bayyana taron a matsayin mai dimbin tarihi, saboda yadda ya tabbatar da aniyar Gwamna Lalong na janyo hankalin jama’ar jihar domin watsi da matsalolin da aka samu a baya dan rungumar zaman lafiya.

Cikin wadanda suka halarci bikin har da tsofaffin gwamnonin Jihar, Janar Lawrence Onoja mai ritaya da Sir Fidelis Tapgun.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Jihar FilatoJosLalongRikicin KabilanciSarkin KanoSarkin MusulmiTaron Yafiya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotun Koli Ta Dakatar Da Daina Amfani Da Tsofaffin Kudi Na Wucin Gadi

Next Post

2023: Mun Fara Horas Da Ma’aikatan Wucin-gadi Miliyan 1.2 – INEC

Related

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

5 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

14 hours ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

16 hours ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

16 hours ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

1 day ago
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

2 days ago
Next Post
2023: Mun Fara Horas Da Ma’aikatan Wucin-gadi Miliyan 1.2 – INEC

2023: Mun Fara Horas Da Ma'aikatan Wucin-gadi Miliyan 1.2 - INEC

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.