• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dan Takarar Gwamnan ZLP A Bauchi Ya Musanta Janye Takararsa

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Siyasa
0
Dan Takarar Gwamnan ZLP A Bauchi Ya Musanta Janye Takararsa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar ZLP a Jihar Bauchi, ta bukaci babban lauya, Eko Ejembi (SAN) da abokan aikinsa da su fara shirye-shiryen daukar matakan shari’a kan kwamitin yakin zaben shugaban kasa na jam’iyyar PDP bisa bayyana cewa dan takarar jam’iyyar a Jihar Bauchi, Ambasada Khalid Arewa ya koma PDP tare da janye takararsa.

Idan ba a manta ba a ranar Talata kwamitin yakin zaben shugaban kasa na jam’iyyar PDP, ya ziyarci Jihar Bauchi domin yakin zabensa, inda kusoshi na jam’iyyar ciki har da dan takarar shugaban kasa, Atiku Abubakar da gwamna Bala Muhammad suka halarta, inda aka bayyana sunayen wasu da suka koma PDP ciki har da ayyana sunan dan takarar gwamna na jam’iyyar ZLP.

  • Ya Kamata Amurka Ta Sauya Mahangar Ta Game Da Sin
  • Na Yi Alkawari Zan Kawar Da Matsalolin Al’umma, In Ji Tinubu

A hirarsa da LEADERSHIP Hausa a ranar Alhamis, dan takarar, ya karyata labarin, ya kuma nuna bacin ransa tare da cewa kwata-kwata babu wanda ya tuntubesa kan wannan zance.

“Ina zaune a ofis ina ganawa da wasu sai aka fara kirana a waya ana tambayata, ya aka yi aka ji sunana cewa na koma PDP?

“Na ce ban gane ba, wace magana ce wannan?. Wasa gaske na amsa kiran waya kan wannan batun a lokacin sama da 100, inda magoya bayanmu suna nuna takaicinsu da nuna bacin ransu da jin wannan maganar.

Labarai Masu Nasaba

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

“Gaskiya ni ban san da wannan batu ba kuma ba a yi wannan zancen da ni ba. Kuma ba mu shirya cewa zan sauya sheka na koma wata jam’iyya ba.

“Kowa ya ga yadda muka karbu a Jihar Bauchi, babu wani matashi kamata a duk ‘yan takarar nan, ni ne mai karancin shekaru kuma matasa suna alfahari da hakan. Sun kuma shirya wajen ganin nasu ya karbi mulki. Alhamdullahi muna kallon nasara domin tsakaninmu idan har aka yi zabe bisa gaskiya to ni zan ci, sai dai idan magudi za a yi.”

Ya ce, ya fito ya barranta kansa da wannan ikirarin da PDP da ‘yan takaranta suka yi a gaban dubban jama’a.

“Na rubuta wasika zuwa ga babban lauya na kasa kuma muna jiran amsarsa, domin ka san mai neman shugaban kasa zan yi kara Atiku Abubakar da Dino Melaye da ya kira sunana, da kuma shugaban jam’iyyar PDP na kasa Iyorchia Ayu, da shugaban PDP na Jihar Bauchi, Hamza Koshe Akuyam.”

Arewa, ya sha alwashin samun nasara a zaben gwamna na 11 ga watan Maris, 2023.

“Wannan bata suna ne baro-baro a matsayina na dan takarar gwamna da nake kallon zan ci zabe, yanzu a sakamakon wannan furucin da suka yi na rasa akalla kashi 30 na magoya bayana.

“Wani daga jin wannan batun shi ke nan ya tafi da shi a ransa ke nan, wani kuma zai ga tun farko yaudararsa aka yi, wani kuma zai ga ban kyauta wa masoyana ba, kowa da yadda zai dauki batun, don haka ba lamari ne da za mu bar shi haka nan ba.”

Arewa ya ce, kwata-kwata babu wata yarjejeniya da suka yi da gwamnatin Jihar Bauchi ko PDP kan cewa zai janye takararsa ba.

“Idan ma za mu janye ya kamata a ji nunfashinmu balle ma hakan baya daga cikin manufarmu. Shin an ma fito an fadi hakan a kan mu don an fi mu cancanta ne ko don rainin da aka mana? Ko kuma a’a fahimtarmu ce ta zo daya, amma babu haka kawai mutum ya tashi kawai ya ce mun janye neman takararmu hakan ba za ta yiwuwa ba.”

A kwafin wasikar da ZLP ta aike wa Lauyoyin ta ce, “Daukan matakin shari’ar shi ne zai dawo wa jam’iyyarmu da kima da mutuncinta kan yarfen da aka mana.”

Wasikar mai dauke da sanya hannun Ambasada Khalid Arewa, dan takarar gwamna na jam’iyyar, “Kwasam a ranar 7 ga watan Fabrairu, 2023 PDP-PCC ya kira sunan dan takarar gwamnanmu a jihar Bauchi, Ambasada Khalid Arewa da cewa ya koma jam’iyyar PDP, wannan furucin ya janyo mana asara sosai da jawo damuwa.”

“Tun lokacin da PDP ta fito ta yi wannan furucin, magoya baya da masoyan ZLP sun shiga damuwa sun kuma nuna rashin jin dadinsu a sassa daban-daban na kananan hukumomin jihar Bauchi.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArewaBauchiSiyasaZLP
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Kamata Amurka Ta Sauya Mahangar Ta Game Da Sin

Next Post

Sin Ta Ba Da Agajin Kayayyakin Aikin Jinya Ga Syria

Related

Labarai

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

1 day ago
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC
Labarai

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

1 day ago
Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 
Siyasa

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

3 days ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

4 days ago
Hoton Kwankwaso da Ganduje da Shekarau
Bakon Marubuci

Daga Sawaba Zuwa Asara: Baje Kolin Kasuwancin Siyasa A Kano – Auwalu Anwar

6 days ago
Na Yafe Wa Buhari Duk Abin Da Ya Min – Buba Galadima
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ci Amanar Kano, Babu Batun Haɗin Guiwa Tsakaninsa Da Kwankwaso A 2027 – Galadima

7 days ago
Next Post
Sin Ta Ba Da Agajin Kayayyakin Aikin Jinya Ga Syria

Sin Ta Ba Da Agajin Kayayyakin Aikin Jinya Ga Syria

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.