• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwamishinan Kasafin Kudin Jihar Zamfara Ya Bar APC Ya Koma PDP

by Bello Hamza
3 years ago
in Siyasa
0
Kwamishinan Kasafin Kudin Jihar Zamfara Ya Bar APC Ya Koma PDP
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamishinan kasafin kudi a Zamfara ya saki tafiyar APC, ya kama jam’iyyar PDP mai adawa gabanin zaben 2023.

Alhaji Aliyu ya bayyana cewa, ba zai ci gaba da zama a jam’iyyar da gazawarta ta fi nasararta yawa ba, tuni dan takarar gwamnan jihar Zamfara a PDP ya karbi kwamishinan tare da bayyana kwarin gwiwa a zaben bana.

  • PDP Ta Kori Nnamani, Ogbu, Dan Fayose, Da Wasu Daga Jam’iyyar
  • Mataimakin Gwamnan Sakkwato, Dan Iya, Ya Musanta Ficewa Daga PDP

Sabon rikici na kunno kai a jam’iyyar APC a jihar Zamfara yayin da kwamishinan gwamna Muhammad Bello Matawalle ya sauya sheka zuwa jam’iyyar PDP.

Kwamishinan kasafin kudi da tattalin arziki, Alhaji Aliyu Tukur E.S Mafara a wani taron ‘yan jarida a Gasau a ranar Juma’a ya ce ya bar jam’iyyar APC tare da komawa PDP; ya marawa dan takarar gwamnan PDP a jihar, Dauda Lawal.

Alhaji Mafara na daya daga cikin jiga-jigan jam’iyyar APC a jihar Zamfara kuma yana daga cikin masu fada a ji a siyasar jihar, LEADERSHIP ta ruwaito.

Labarai Masu Nasaba

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Da yake magana bayan ganawa da dan takarar gwamnan na PDP, tsohon kwamishinan ya jaddada cewa, ba zai bari ya ci gaba da zama a inda abu ya ki gaba ya ki baya ba.

A cewarsa: “Na sanar da gwamnatin jihar, tsohon gwamna da kuma mabiya bayana gabanin sauya sheka daga APC zuwa PDP.

“Ina yin wannan ne saboda mutane na, kuma ina da yakini kan Dr. Dauda Lawal, idan aka ba shi dama ya zama gwamnan Zamfara a zabe mai zuwa, zai shawo kan matsalolin tsaro, ya habaka harkar noma, ya samar da kasuwanni masu kyau ga manoma.

“Saboda haka, na ba da dukkan goyon baya na ga jam’iyyar PDP, kuma ina son yin kira ga magoya bayana a Zamfara da su bi tafiyar Dauda Lawal da PDP a zabe mai zuwa.”

Dan takarar gwamnan PDP ya magantu A nasa bangaren, dan takarar gwamnan jihar Zamfara na PDP, Dauda Lawal, ya tabbatar da cewa, Zamfara jiha ce ta PDP, inda ya kara da cewa, jam’iyyar za ta sake samun nasarar karbe mulki a zaben 2023.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bashin Dala Miliyan 350 Da Kaduna Ta Ciyo: Nasara Ko Akasinta?

Next Post

Gakpo Ya Yi Gaggawar Koma Wa Liverpool, Cewar Koeman

Related

Labarai

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

1 day ago
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC
Labarai

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

1 day ago
Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 
Siyasa

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

4 days ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

4 days ago
Hoton Kwankwaso da Ganduje da Shekarau
Bakon Marubuci

Daga Sawaba Zuwa Asara: Baje Kolin Kasuwancin Siyasa A Kano – Auwalu Anwar

6 days ago
Na Yafe Wa Buhari Duk Abin Da Ya Min – Buba Galadima
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ci Amanar Kano, Babu Batun Haɗin Guiwa Tsakaninsa Da Kwankwaso A 2027 – Galadima

7 days ago
Next Post
Gakpo Ya Yi Gaggawar Koma Wa Liverpool, Cewar Koeman

Gakpo Ya Yi Gaggawar Koma Wa Liverpool, Cewar Koeman

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.