ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gakpo Ya Yi Gaggawar Koma Wa Liverpool, Cewar Koeman

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Gakpo

Kociyan tawagar kasar Netherlands, Ronald Koeman ya ce Cody Gakpo ya yi saurin koma wa Liverpool bayan ya kasa taka rawa a kungiyar da ke fuskantar kalubale a bana.

Mai shekara 23 ya taka rawar gani a gasar kofin duniya a Katar da cin kwallo uku a wasa biyar, bayan da Netherlands ta kai wasan kusa dana kusa dana karshe a gasar da Argentina ta yi waje da su.

  • Ba Zan Bar Liverpool Ba Sai Dai A Kore Ni, Cewar Klopp

Sai dai ya kasa cin kwallo a wasanni shida a Liverpool, tun bayan da ya koma daga PSB Eindhoben a watan Janairu bayan da farko kungiyar Manchester United ta yi zawarcinsa.

ADVERTISEMENT

Koeman ya ce ”Ya koma kungiyar da ba ta yin kokari a kakar nan kuma abu ne mai dan karen wahala a makomar dan wasa matashi da baya cin kwallo, kuma kungiya ba ta cin wasanni, sannan ba a ganin mahimmanci ka.”

Ya kara da cewa ”Idan dan wasa ne da ya kai shekara 28 mai dinbin kwarewa, abin zai zama na daban.”

LABARAI MASU NASABA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

Koeman tsohon kociyan Everton, wanda ke jan ragamar Netherlands karo na biyu ya ce matashin dan wasan Netherlands kan fuskanci kalubale idan ya koma fitatciyar kungiya.

Kafin Gakpo ya koma Liverpool ya ci kwallo tara ya bayar da 12 aka zura a raga a wasa 14 a PSB a kakar bana a babbar gasar kasar Netherlands sai dai Liverpool, wadda aka fitar da ita daga Carabao da FA Cup a bana tana ta 10 a teburin Premier League da maki 29, za ta kara da Real Madrid a Champions League.

Liverpool ta yi rashin nasara da ci 3-0 a hannun Wolberhampton a wasan mako na 22 a gasar Premier League a satin daya gabata kuma da wannan sakamakon Liverpool , wadda ta yi wasa 20 tana ta 10 a teburin firimiyar Ingila da maki 29.

Wasa na bakwai kenan da Liverpool ta kara a shekara 2023, kuma daya daga ciki tayi nasara shi ne a FA Cup da ta doke Wolbes 1-0 to sai dai har yanzu Liverpool ba ta karawa ba a gasar Premier a 2023 a wasa hudun da ta fafata kawo yanzu.

Jerin wasannin da Liverpool ta buga a 2023:
Premier League Litinin 2 ga watan Janairu Brentford 3 – 1 Liverpool FA CUP Asabar 7 ga watan Janairu Liverpool 2 – 2 Wolbes Premier League Sa 14 ga Jan 2023 Brighton 3 – 0 Liverpool

FA CUP Talata 17 ga watan Janairu Wolbes 0 – 1 Liverpool Premier League Asabar 21 ga watan Janairu Liverpool 0 – 0 Chelsea FA CUP Lahadi 29 ga watan Janairu Brighton 2 – 1 Liverpool Premier League Asabar 4 ga watan Janairu Wolves 3 – 0 Liverpool Wasa uku na gaba da Liverpool za ta buga Premier League Litinin 13 ga watan Fabrairu Liverpool da Everton Premier League Asabar 18 ga watan Fabrairu Newcastle da Liverpool Champions League Talata 21 ga watan Fabrairu. Liverpool da Real Madrid.

Gakpo
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?
  • Abba Ibrahim Wada
    Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji
  • Abba Ibrahim Wada
    Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City

MASU ALAKA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
Wasanni

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
Wasanni

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Wasanni

Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu

July 11, 2026
Next Post
Tasirin Karancin Kudade Ga Kananan Sana’o’i

Tasirin Karancin Kudade Ga Kananan Sana’o’i

LABARAI MASU NASABA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.