ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gakpo Ya Yi Gaggawar Koma Wa Liverpool, Cewar Koeman

by Abba Ibrahim Wada
4 years ago
Gakpo

Kociyan tawagar kasar Netherlands, Ronald Koeman ya ce Cody Gakpo ya yi saurin koma wa Liverpool bayan ya kasa taka rawa a kungiyar da ke fuskantar kalubale a bana.

Mai shekara 23 ya taka rawar gani a gasar kofin duniya a Katar da cin kwallo uku a wasa biyar, bayan da Netherlands ta kai wasan kusa dana kusa dana karshe a gasar da Argentina ta yi waje da su.

  • Ba Zan Bar Liverpool Ba Sai Dai A Kore Ni, Cewar Klopp

Sai dai ya kasa cin kwallo a wasanni shida a Liverpool, tun bayan da ya koma daga PSB Eindhoben a watan Janairu bayan da farko kungiyar Manchester United ta yi zawarcinsa.

ADVERTISEMENT

Koeman ya ce ”Ya koma kungiyar da ba ta yin kokari a kakar nan kuma abu ne mai dan karen wahala a makomar dan wasa matashi da baya cin kwallo, kuma kungiya ba ta cin wasanni, sannan ba a ganin mahimmanci ka.”

Ya kara da cewa ”Idan dan wasa ne da ya kai shekara 28 mai dinbin kwarewa, abin zai zama na daban.”

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

Koeman tsohon kociyan Everton, wanda ke jan ragamar Netherlands karo na biyu ya ce matashin dan wasan Netherlands kan fuskanci kalubale idan ya koma fitatciyar kungiya.

Kafin Gakpo ya koma Liverpool ya ci kwallo tara ya bayar da 12 aka zura a raga a wasa 14 a PSB a kakar bana a babbar gasar kasar Netherlands sai dai Liverpool, wadda aka fitar da ita daga Carabao da FA Cup a bana tana ta 10 a teburin Premier League da maki 29, za ta kara da Real Madrid a Champions League.

Liverpool ta yi rashin nasara da ci 3-0 a hannun Wolberhampton a wasan mako na 22 a gasar Premier League a satin daya gabata kuma da wannan sakamakon Liverpool , wadda ta yi wasa 20 tana ta 10 a teburin firimiyar Ingila da maki 29.

Wasa na bakwai kenan da Liverpool ta kara a shekara 2023, kuma daya daga ciki tayi nasara shi ne a FA Cup da ta doke Wolbes 1-0 to sai dai har yanzu Liverpool ba ta karawa ba a gasar Premier a 2023 a wasa hudun da ta fafata kawo yanzu.

Jerin wasannin da Liverpool ta buga a 2023:
Premier League Litinin 2 ga watan Janairu Brentford 3 – 1 Liverpool FA CUP Asabar 7 ga watan Janairu Liverpool 2 – 2 Wolbes Premier League Sa 14 ga Jan 2023 Brighton 3 – 0 Liverpool

FA CUP Talata 17 ga watan Janairu Wolbes 0 – 1 Liverpool Premier League Asabar 21 ga watan Janairu Liverpool 0 – 0 Chelsea FA CUP Lahadi 29 ga watan Janairu Brighton 2 – 1 Liverpool Premier League Asabar 4 ga watan Janairu Wolves 3 – 0 Liverpool Wasa uku na gaba da Liverpool za ta buga Premier League Litinin 13 ga watan Fabrairu Liverpool da Everton Premier League Asabar 18 ga watan Fabrairu Newcastle da Liverpool Champions League Talata 21 ga watan Fabrairu. Liverpool da Real Madrid.

Gakpo
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Yaushe Za A Fara Kofin Zakarun Turai
  • Abba Ibrahim Wada
    Messi Ya Yi Ritaya A Argentina: Da Me Za Mu Iya Tuna Gwarzon Duniyar?
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye ‘Yan wasan Nijeriya Da Za Su Buga Gasar Firimiyar Ingila Ta Bana?
  • Abba Ibrahim Wada
    Chelsea A Ƙarƙashin Xavi Alonso

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
Wasanni

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

September 8, 2026
Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
Wasanni

Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain

September 7, 2026
Next Post
Tasirin Karancin Kudade Ga Kananan Sana’o’i

Tasirin Karancin Kudade Ga Kananan Sana’o’i

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.