• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsohon Daraktan Yakin Neman Zaben Tsohon Gwamnan Bauchi Ya Koma Labour Party

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Siyasa
0
Tsohon Daraktan Yakin Neman Zaben Tsohon Gwamnan Bauchi Ya Koma Labour Party
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon daraktan yakin zaben tsohon gwamnan jihar Bauchi, Muhammadu Abdullahi Abubakar, wato Alhaji Garba Sarki Akuyam, ya shelanta ficewa daga jam’iyyar APC tare komawa cikin jam’iyyar Labour Pary (LP) tare da daruruwan magoya bayansa.

Akuyam wanda tsohon kwamishinan kudi da ci gaban tatttalin arziki na jihar Bauchi ne, ya shelanta komawa LP ne a ziyarar da ya kai wa shugaban jam’iyyar a jihar Bauchi, Barista Hussaini Saraki a ofishin jam’iyyar jiya, yana mai cewa, ya tuntubi masu ruwa da tsaki da magoya bayansa kafin daukan wannan matakin.

  • ‘Yan Jihar Bauchi Sun Yabawa Buhari Kan Amincewa Da Ci Gaba Da Amfani Da Tsohuwar 200
  • Dan Takarar Gwamnan ZLP A Bauchi Ya Musanta Janye Takararsa

Akuyam ya bayyana cewar dalilansa na ficewa daga cikin APC sun hada har da rashin gamsuwarsa da yadda ake gudanar da lamura a cikin jam’iyyar a matakin jiha da ma kasa, kana ya bibiyi tarihin Peter Obi da irin nasarorin da ya cimma a rayuwarsa, don haka yana da kwarin guiwar Peter zai iya shawo kan matsalolin da suke addabar kasar nan.

Ya kara da cewa a matsayinsa na wanda ya ke da gogewa a bangaren siyasa da jagoranci a jam’iyyar APC har ta kai ga samun nasara a zaben 2015 da ya gudana a jihar Bauchi, bai gamsu da yadda ake tafiyar da lamura a cikin jam’iyyar ba a halin yanzu, don haka shi da daruruwan magoya bayansa suka fice daga cikin jam’iyyar.

Ya kuma kara da cewa, abokin takarar Peter, Yusuf Datti Baba Ahmed, ya fito daga fitacciyar zuri’a a arewa kuma yana da kyakkyawar alaka da su, don haka ya ga dacewar ya koma cikin jam’iyyar LP domin bada tashi gudunmawar wajen ganin sun samu nasarar lashe zabukan da ke tafe.

Labarai Masu Nasaba

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Babu Wanda Ya Buƙaci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC

Garba Sarki Akuyam tsohon kwamishinan bunkasa yankunan karkara na jihar Bauchi ne, ya bada tabbacin cewa zai yi dukkanin mai yiyuwa domin ganin nasarar jam’iyyar a dukkanin matakai, ya kuma nemi alfarmar jagororin jam’iyyar da su amince da shi hannu biyu-biyu.

A jawabinsa na maraba, shugaban jam’iyyar Labour Party a jihar Bauchi, Barista Hussaini Saraki, ya shaida cewar wannan babban nasara ce a garesu kuma yana mai bai wa Akuyam da sauran magoya bayansa tabbacin samun adalci a jam’iyyar.

“Tabbas samun kwararren masanin siyasa kuma masanin tattalin arziki a cikin jam’iyyarmu babban nasara ce a garemu. Sannan, yadda jama’a suke tururuwar shigowa cikin LP a jihar Bauchi na nuna mana irin gagarumar nasarar da za mu iya samu a zaben da ke tafe.”

Ya kuma nuna kwarin guiwarsa na samun nasarar jam’iyyar a dukkanin matakai, yana mai kira ga sauran jama’a da su shigo a dama da su domin ceto kasar nan daga halin da take ciki.

Saraki daga bisani ya jinjina wa Sarkin Akuyam bisa daukar wannan matakin fi dacewa domin hada karfi da karfe wajen ceto Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jami’in MDD: Fasahohin Sin Za Su Taimaka Wa Afirka Tinkarar Matsalar Sauyin Yanayi

Next Post

An Bude Baje Kolin Fina-finai Kan Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”

Related

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta
Labarai

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

19 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Siyasa

Babu Wanda Ya Buƙaci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC

2 days ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027

3 days ago
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC
Labarai

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

4 days ago
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista
Da ɗumi-ɗuminsa

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

4 days ago
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC
Da ɗumi-ɗuminsa

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

5 days ago
Next Post
An Bude Baje Kolin Fina-finai Kan Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”

An Bude Baje Kolin Fina-finai Kan Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa

July 11, 2025
Goron Sallah

GORON JUMA’A

July 11, 2025
An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

July 11, 2025
Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

July 11, 2025
Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

July 11, 2025
NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

July 11, 2025
Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

July 11, 2025
NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

July 11, 2025
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

July 11, 2025
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.