• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben 2023: Na’urar BVAS Ta Ki Tantance Yakubu Dogara

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Zaben 2023: Na’urar BVAS Ta Ki Tantance Yakubu Dogara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Na’urar tantance masu zabe wato BVAS, ta gaza daukan zanen yatsu da hoton fuskar tsohon kakakin Majalisar Dokokin Tarayya, Hon. Yakubu Dogara.

Dogara wanda ya je rumfar zabensa da ke Kauyen Kwarangah da ke karamar hukumar Bogoro a rumfar mai lamba 007 tun wajen 10 na safiya har zuwa 2:pm amma na’urar ta kasa tantance shi balle ya samu damar jefa kuri’arsa.

  • PDP Za Ta Kai Ga Nasara -Tambuwal
  • Ina Da Kwarin Guiwar Lashe Zabe -Tinubu

Lamarin dai ya sanya shi zaman dirshen kawai a wajen zaben da jiran ko na’urar za ta sahaleshi.

Da ya ke zantawa da ‘yan jarida kan wannan matakin, Yakubu Dogara ya nuja takaicinsa na cewa na’urar BVAS guda daya tak ke aiki a mazabar duk da cewa masu zabe sun kusan kaiwa mutum 2,000 a wajen.

Kazalika ya shaida cewar wasu ma da dama na’urar ta kasa tantance su don haka ya yi zargin cewa ana shirin fusata jama’a har su koma gidajensu ba tare da yin zaben ba.

Labarai Masu Nasaba

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

Dogara ya ce, lokacin da ya zo na’urar ba ta tantance shi ba, ya garzaya ofishin INEC da ke karamar hukumar Bogoro domin neman bahasin yadda aka dauki BVAS din Kwaranga zuwa karamar hukumar Tafawa Balewa.

Ya nuna takaicinsa kan yadda al’umma suka bar gidajensu suka fito domin kada kuri’a amma na’urar ta ki tantance su, “Ana ta kan ba da hakuri wa jama’a, to amma muna ganin takaici ne, an ce mana BVAS machine din nan da aka ce ko ma ina ko inda babu network zai yi aiki. Yanzu mun zo an ce ba ta aiki, an dauka an kai Tafawa Balewa, gari da ke da nisan kilomita 12 zuwa 13 daga inda muke a yau don a je a samu network.

“Amma abun da za a lura da shi a nan kasar Kwarangah akwai network masu karfi guda biyu na MTN da Glo. Damuwar mu shi ne meye sa za a dauki BVAS na Kwarangah a kai shi Tafawa Balewa domin a gyara, ko ma network din bai da karfi ai akwai network a Bogoro.

Ya ce, baya ga wannan duk rumfar jefa kuri’ar da ke masu zabe sama da dubu biyu ya kamata a basu BVAS guda hudu, “Amma sun kawo biyu kacal nan duk da masu zabenmu sun kusan dubu biyu. A cikin biyun da suka kawo ma 1 baya aiki. Don haka muna ganin wannan kamar ana son a kular da mutane ne su yi fushi su koma gidaje su ce ba za su yi zabe ba.”

Ya ce za su cigaba da jiran abubuwan da jami’an INEC za su yi domin su na son kada kuri’arsu.

Ya nuna takaicinsa kan yadda na’urar ke cigaba da haifar da koma baya ga zaben.

Daga bisani Dogara ya yi amfani da damar wajen neman jama’a da su yi zabe cikin kwanciyar hankali kuma ya nemi masu takara da su dauki aniyar amsar sakamakon zaben da za a bayyana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BVASYakubu DogaraZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

PDP Za Ta Kai Ga Nasara -Tambuwal

Next Post

Faduwar Farashin Kaudar Tumatir Zai Rage Wa Manoma Karfin Gwiwa

Related

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

32 minutes ago
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

5 hours ago
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

9 hours ago
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa
Manyan Labarai

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

9 hours ago
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

10 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

13 hours ago
Next Post
Faduwar Farashin Kaudar Tumatir Zai Rage Wa Manoma Karfin Gwiwa

Faduwar Farashin Kaudar Tumatir Zai Rage Wa Manoma Karfin Gwiwa

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.