ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben 2023: Na’urar BVAS Ta Ki Tantance Yakubu Dogara

by Khalid Idris Doya
3 years ago
BVAS

Na’urar tantance masu zabe wato BVAS, ta gaza daukan zanen yatsu da hoton fuskar tsohon kakakin Majalisar Dokokin Tarayya, Hon. Yakubu Dogara.

Dogara wanda ya je rumfar zabensa da ke Kauyen Kwarangah da ke karamar hukumar Bogoro a rumfar mai lamba 007 tun wajen 10 na safiya har zuwa 2:pm amma na’urar ta kasa tantance shi balle ya samu damar jefa kuri’arsa.

  • PDP Za Ta Kai Ga Nasara -Tambuwal
  • Ina Da Kwarin Guiwar Lashe Zabe -Tinubu

Lamarin dai ya sanya shi zaman dirshen kawai a wajen zaben da jiran ko na’urar za ta sahaleshi.

ADVERTISEMENT

Da ya ke zantawa da ‘yan jarida kan wannan matakin, Yakubu Dogara ya nuja takaicinsa na cewa na’urar BVAS guda daya tak ke aiki a mazabar duk da cewa masu zabe sun kusan kaiwa mutum 2,000 a wajen.

Kazalika ya shaida cewar wasu ma da dama na’urar ta kasa tantance su don haka ya yi zargin cewa ana shirin fusata jama’a har su koma gidajensu ba tare da yin zaben ba.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Dogara ya ce, lokacin da ya zo na’urar ba ta tantance shi ba, ya garzaya ofishin INEC da ke karamar hukumar Bogoro domin neman bahasin yadda aka dauki BVAS din Kwaranga zuwa karamar hukumar Tafawa Balewa.

Ya nuna takaicinsa kan yadda al’umma suka bar gidajensu suka fito domin kada kuri’a amma na’urar ta ki tantance su, “Ana ta kan ba da hakuri wa jama’a, to amma muna ganin takaici ne, an ce mana BVAS machine din nan da aka ce ko ma ina ko inda babu network zai yi aiki. Yanzu mun zo an ce ba ta aiki, an dauka an kai Tafawa Balewa, gari da ke da nisan kilomita 12 zuwa 13 daga inda muke a yau don a je a samu network.

“Amma abun da za a lura da shi a nan kasar Kwarangah akwai network masu karfi guda biyu na MTN da Glo. Damuwar mu shi ne meye sa za a dauki BVAS na Kwarangah a kai shi Tafawa Balewa domin a gyara, ko ma network din bai da karfi ai akwai network a Bogoro.

Ya ce, baya ga wannan duk rumfar jefa kuri’ar da ke masu zabe sama da dubu biyu ya kamata a basu BVAS guda hudu, “Amma sun kawo biyu kacal nan duk da masu zabenmu sun kusan dubu biyu. A cikin biyun da suka kawo ma 1 baya aiki. Don haka muna ganin wannan kamar ana son a kular da mutane ne su yi fushi su koma gidaje su ce ba za su yi zabe ba.”

Ya ce za su cigaba da jiran abubuwan da jami’an INEC za su yi domin su na son kada kuri’arsu.

Ya nuna takaicinsa kan yadda na’urar ke cigaba da haifar da koma baya ga zaben.

Daga bisani Dogara ya yi amfani da damar wajen neman jama’a da su yi zabe cikin kwanciyar hankali kuma ya nemi masu takara da su dauki aniyar amsar sakamakon zaben da za a bayyana.

BVAS
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Faduwar Farashin Kaudar Tumatir Zai Rage Wa Manoma Karfin Gwiwa

Faduwar Farashin Kaudar Tumatir Zai Rage Wa Manoma Karfin Gwiwa

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.