ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben 2023: Na’urar BVAS Ta Ki Tantance Yakubu Dogara

by Khalid Idris Doya
3 years ago
BVAS

Na’urar tantance masu zabe wato BVAS, ta gaza daukan zanen yatsu da hoton fuskar tsohon kakakin Majalisar Dokokin Tarayya, Hon. Yakubu Dogara.

Dogara wanda ya je rumfar zabensa da ke Kauyen Kwarangah da ke karamar hukumar Bogoro a rumfar mai lamba 007 tun wajen 10 na safiya har zuwa 2:pm amma na’urar ta kasa tantance shi balle ya samu damar jefa kuri’arsa.

  • PDP Za Ta Kai Ga Nasara -Tambuwal
  • Ina Da Kwarin Guiwar Lashe Zabe -Tinubu

Lamarin dai ya sanya shi zaman dirshen kawai a wajen zaben da jiran ko na’urar za ta sahaleshi.

ADVERTISEMENT

Da ya ke zantawa da ‘yan jarida kan wannan matakin, Yakubu Dogara ya nuja takaicinsa na cewa na’urar BVAS guda daya tak ke aiki a mazabar duk da cewa masu zabe sun kusan kaiwa mutum 2,000 a wajen.

Kazalika ya shaida cewar wasu ma da dama na’urar ta kasa tantance su don haka ya yi zargin cewa ana shirin fusata jama’a har su koma gidajensu ba tare da yin zaben ba.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Dogara ya ce, lokacin da ya zo na’urar ba ta tantance shi ba, ya garzaya ofishin INEC da ke karamar hukumar Bogoro domin neman bahasin yadda aka dauki BVAS din Kwaranga zuwa karamar hukumar Tafawa Balewa.

Ya nuna takaicinsa kan yadda al’umma suka bar gidajensu suka fito domin kada kuri’a amma na’urar ta ki tantance su, “Ana ta kan ba da hakuri wa jama’a, to amma muna ganin takaici ne, an ce mana BVAS machine din nan da aka ce ko ma ina ko inda babu network zai yi aiki. Yanzu mun zo an ce ba ta aiki, an dauka an kai Tafawa Balewa, gari da ke da nisan kilomita 12 zuwa 13 daga inda muke a yau don a je a samu network.

“Amma abun da za a lura da shi a nan kasar Kwarangah akwai network masu karfi guda biyu na MTN da Glo. Damuwar mu shi ne meye sa za a dauki BVAS na Kwarangah a kai shi Tafawa Balewa domin a gyara, ko ma network din bai da karfi ai akwai network a Bogoro.

Ya ce, baya ga wannan duk rumfar jefa kuri’ar da ke masu zabe sama da dubu biyu ya kamata a basu BVAS guda hudu, “Amma sun kawo biyu kacal nan duk da masu zabenmu sun kusan dubu biyu. A cikin biyun da suka kawo ma 1 baya aiki. Don haka muna ganin wannan kamar ana son a kular da mutane ne su yi fushi su koma gidaje su ce ba za su yi zabe ba.”

Ya ce za su cigaba da jiran abubuwan da jami’an INEC za su yi domin su na son kada kuri’arsu.

Ya nuna takaicinsa kan yadda na’urar ke cigaba da haifar da koma baya ga zaben.

Daga bisani Dogara ya yi amfani da damar wajen neman jama’a da su yi zabe cikin kwanciyar hankali kuma ya nemi masu takara da su dauki aniyar amsar sakamakon zaben da za a bayyana.

BVAS
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Faduwar Farashin Kaudar Tumatir Zai Rage Wa Manoma Karfin Gwiwa

Faduwar Farashin Kaudar Tumatir Zai Rage Wa Manoma Karfin Gwiwa

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.