ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Faduwar Farashin Kaudar Tumatir Zai Rage Wa Manoma Karfin Gwiwa

by Abubakar Abba
3 years ago
Tumatir

Kaudar tumatur na daga cikin hanyar da manoma kan bi wajen adana tumaturi domin yin amfani da shi a lokacin da babau danye, musamman a lokacin bazara ko kuma tsakiyar damuna.

Akwai wurare daban-daban da ake noman tumatur a fadin kasar nan a lokacin rani, Kwanar-gafan da ke karamar hukumar Garun-malam, a jihar Kano na daga cikin manyan kasuwannin tumatur a fadin kasar nan, wadda ake zuwa daga sassa daban-daban domin yin kasuwcin tumaturin.

  • Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Matsayinta Na Warware Matsalar Ukraine A Siyasance
  • Shawarwarin Dattawan Arewa Kan Zaben 2023

Ana kai tumaturin zuwa sassa daban-daban na kasar nan, har ma zuwa makotanmu. Manoman wannan yanki na kai tumaturin nasu wannan kasuwa, domin su sayar.

ADVERTISEMENT

Kasuwar na daga cikin kasuwannanin da ke samar da hada-hadar kasuwanci ga dimbin al’umma daga sassa daban-daban na kasar nan.

Bayan hada-hadar kasuwancin danyen tumaturin akwai wadanda ke hada-hadar kasuwancin kaudarsa, wato busasshensa ke nan.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Mayar da tumaturin zuwa kauda na taimaka wa manomansa rage asara, musamman idan suka daure, suka adana shi zuwa wani lokaci,wato, lokacin farkon damuna, kafin na damuna ya fara shigo wa.

Sai dai duk da haka, a kan yi hada-hadar kasuwancin kaudar tumaturin tun daga lokacin da aka fara shanya shi.

A bana musamman halin da aka shiga na sauyin kudi, ya dakile kasuwar tumatur yadda manomansa suka yi dimbin asara. Masu nomansa da masu kasuwancinsa sun shiga halin tsaka-mai-wuya, saboda matsalar kudin da za yi amfani da su wajen yin safarar ta sa. Wannan ta sa dole manoman suka shiga shanya tumaturin nasu, tunda babu kasuwa.

A makwanni biyu da suka wuce a kasuwar kwanan-gafan babbar kasuwar tumaturin ta Kwanar-gafan kasuwar tunatur ta fadi kasa warwas, inda manoma ke sayar da katon Kwando a kan naira dubu biyu zuwa naira dubu biyu da dari biyar, wannan ta sa yawan masu shanyarsa ya karu. Karuwar masu shanyar ta sa farashin busassahen tumaturin ya fadi kasa warwas.

Duk da cewa, a daidai wannan loacin, lokaci ne na ganiyar samun kaudar tumaturin, kuma yakan yi sauki matuka, wanda har masu sari kan saya su adana shi, to amma a bana faduwar farashin ta yi kasa sosai, saboda wanda yakamata a sayar da shi kuma a yi amfani da shi tun yana danye, yanayi ya sa hakan ba ta yiwu ba.

Manoman tumarurin dai sun koka matuka da faduwar farashin, domin yana taimaka musu wajen samun kudaden yin hidimarsau ta yau da kullum.

Sannan kuma yana taimaka wa manoman wajen yin noman damuna. Saboda haka a bana manoman na tumatur da masu kasuwancin busassahen tumaturin sun shiga halin tsaka-mai-wuya.

Sannan kuma a daidai wannan lokacin da ake sanyi, yawan tumarun da ake diba na karuwa. Ga yawa na karuwa ga farashi na sauka.

Sai dai wani manomi da aka zanta da shi, a kasuwar ta Kwanar-gafan ya tabbatar da cewa, faduwar farashin kaudar tumaturin zai shafi noman damina, domin kudin da suke samu daga noman tumatirin ya ragu kwarai.

Sannan kuma wasu manoman sun bukaci gwamnati da manyan ‘yan kasuwa da su taimaka musu wajen kafa musu masana’antar da za ta sarrafa tumaturin yadda za a iya adana shi, da kuma daukarsa a kai shi sassa daban-daban na ciki da wajen kasar nan. Domin kuwa yin hakan zai taimaka musu wajen rage asarar da suke fuskanta a halin yanzu.

Wani mai kasuwancin kaudar tumaturin da ke zaune a garin Kwanar-dangora, mai suna Sani Bilak, ya koka matuka kan yadda a bana hada-hadar kasuwancin ta su ta samu cikas, wanda ya ce, hakan ta kawo musu cikas matuka.

Don haka, shi ma kiran da nasa ga gwamnati ya yi da manyana ‘yan kasuwa da su samar da hanyar da za a dinga adana tumaturin domin guje wa irin wannan mummunar asara.

Masu shanyar kaudar tumaturin su ma sun ce da gwamnati za ta tallafa musu wajen samar musu da na’urar da za ta busar da tumaturin da an samu saukin yawan asarar da ake yi, sannan kuma zai kasance yana da tsafta, amma a halin yanzu ana sanya shi a wuraen da ba su dace ba. Inda babu cikakkiyar tsafta.

Tumatir
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Zaben 2023: Tinubu Ya Lashe Akwatin Mazabarsa

Zaben 2023: Tinubu Ya Lashe Akwatin Mazabarsa

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.