ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Faduwar Farashin Kaudar Tumatir Zai Rage Wa Manoma Karfin Gwiwa

by Abubakar Abba
3 years ago
Tumatir

Kaudar tumatur na daga cikin hanyar da manoma kan bi wajen adana tumaturi domin yin amfani da shi a lokacin da babau danye, musamman a lokacin bazara ko kuma tsakiyar damuna.

Akwai wurare daban-daban da ake noman tumatur a fadin kasar nan a lokacin rani, Kwanar-gafan da ke karamar hukumar Garun-malam, a jihar Kano na daga cikin manyan kasuwannin tumatur a fadin kasar nan, wadda ake zuwa daga sassa daban-daban domin yin kasuwcin tumaturin.

  • Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Matsayinta Na Warware Matsalar Ukraine A Siyasance
  • Shawarwarin Dattawan Arewa Kan Zaben 2023

Ana kai tumaturin zuwa sassa daban-daban na kasar nan, har ma zuwa makotanmu. Manoman wannan yanki na kai tumaturin nasu wannan kasuwa, domin su sayar.

ADVERTISEMENT

Kasuwar na daga cikin kasuwannanin da ke samar da hada-hadar kasuwanci ga dimbin al’umma daga sassa daban-daban na kasar nan.

Bayan hada-hadar kasuwancin danyen tumaturin akwai wadanda ke hada-hadar kasuwancin kaudarsa, wato busasshensa ke nan.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Mayar da tumaturin zuwa kauda na taimaka wa manomansa rage asara, musamman idan suka daure, suka adana shi zuwa wani lokaci,wato, lokacin farkon damuna, kafin na damuna ya fara shigo wa.

Sai dai duk da haka, a kan yi hada-hadar kasuwancin kaudar tumaturin tun daga lokacin da aka fara shanya shi.

A bana musamman halin da aka shiga na sauyin kudi, ya dakile kasuwar tumatur yadda manomansa suka yi dimbin asara. Masu nomansa da masu kasuwancinsa sun shiga halin tsaka-mai-wuya, saboda matsalar kudin da za yi amfani da su wajen yin safarar ta sa. Wannan ta sa dole manoman suka shiga shanya tumaturin nasu, tunda babu kasuwa.

A makwanni biyu da suka wuce a kasuwar kwanan-gafan babbar kasuwar tumaturin ta Kwanar-gafan kasuwar tunatur ta fadi kasa warwas, inda manoma ke sayar da katon Kwando a kan naira dubu biyu zuwa naira dubu biyu da dari biyar, wannan ta sa yawan masu shanyarsa ya karu. Karuwar masu shanyar ta sa farashin busassahen tumaturin ya fadi kasa warwas.

Duk da cewa, a daidai wannan loacin, lokaci ne na ganiyar samun kaudar tumaturin, kuma yakan yi sauki matuka, wanda har masu sari kan saya su adana shi, to amma a bana faduwar farashin ta yi kasa sosai, saboda wanda yakamata a sayar da shi kuma a yi amfani da shi tun yana danye, yanayi ya sa hakan ba ta yiwu ba.

Manoman tumarurin dai sun koka matuka da faduwar farashin, domin yana taimaka musu wajen samun kudaden yin hidimarsau ta yau da kullum.

Sannan kuma yana taimaka wa manoman wajen yin noman damuna. Saboda haka a bana manoman na tumatur da masu kasuwancin busassahen tumaturin sun shiga halin tsaka-mai-wuya.

Sannan kuma a daidai wannan lokacin da ake sanyi, yawan tumarun da ake diba na karuwa. Ga yawa na karuwa ga farashi na sauka.

Sai dai wani manomi da aka zanta da shi, a kasuwar ta Kwanar-gafan ya tabbatar da cewa, faduwar farashin kaudar tumaturin zai shafi noman damina, domin kudin da suke samu daga noman tumatirin ya ragu kwarai.

Sannan kuma wasu manoman sun bukaci gwamnati da manyan ‘yan kasuwa da su taimaka musu wajen kafa musu masana’antar da za ta sarrafa tumaturin yadda za a iya adana shi, da kuma daukarsa a kai shi sassa daban-daban na ciki da wajen kasar nan. Domin kuwa yin hakan zai taimaka musu wajen rage asarar da suke fuskanta a halin yanzu.

Wani mai kasuwancin kaudar tumaturin da ke zaune a garin Kwanar-dangora, mai suna Sani Bilak, ya koka matuka kan yadda a bana hada-hadar kasuwancin ta su ta samu cikas, wanda ya ce, hakan ta kawo musu cikas matuka.

Don haka, shi ma kiran da nasa ga gwamnati ya yi da manyana ‘yan kasuwa da su samar da hanyar da za a dinga adana tumaturin domin guje wa irin wannan mummunar asara.

Masu shanyar kaudar tumaturin su ma sun ce da gwamnati za ta tallafa musu wajen samar musu da na’urar da za ta busar da tumaturin da an samu saukin yawan asarar da ake yi, sannan kuma zai kasance yana da tsafta, amma a halin yanzu ana sanya shi a wuraen da ba su dace ba. Inda babu cikakkiyar tsafta.

Tumatir
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Zaben 2023: Tinubu Ya Lashe Akwatin Mazabarsa

Zaben 2023: Tinubu Ya Lashe Akwatin Mazabarsa

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.