• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Waiwaye: Konewar Babbar Kasuwar Maiduguri A Shekarar 1979 Da Sake Gina Ta Da Aka Yi A 1983

by Muhammad Bala Garbasu
2 years ago
in Rahotonni
0
‘Yansanda Sun Cafke Mutum 50 Kan Satar Kaya Lokacin Da Gobara Ke Cin Kasuwar Monday Market A Borno
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masu iya magana suka ce waiwaye adon tafiya. Duba da iftila’in gobarar da ya sake samun babbar kasuwar Litinin (Monday market) ta birnin Maiduguri ya sa naga dacewar yin waiwaye izuwa shekaru 44 baya domin sake kawo wa masu karatu wani rohoto da Marigayi Ado Saleh Kankiya ya hada na bude babbar kasuwar Litinin din da aka yi a shekarar 1983 bayan ta kone a shekarar 1979 an sake gina ta.

Wannan rohoton an buga shi a jaridar ‘GASKIYA TA FI KWABO’ a ranar Alhamis 11 ga watan Augusta a shekarar 1983 (har yanzu ina da jaridar). Ga yadda rohoton ya kasance kamar haka:

A RANAR Alhamis, 4/8/83, Gwamnan Jihar Borno, Alhaji Mohammed Goni ya yi bikin bude sabuwar babbar kasuwar Maiduguri wadda aka gina a kan #13 miliyan da sabuwar tashar Telebijin ta Jihar.
Da yake jawabi wajen bude babbar kasuwar, Gwamnan ya yi gargadi ga ‘yan kasuwar da za a rabawa runfunan da su tabbatar da cewar suna biyan kudaden runfunan cikin lokaci.

Alhaji Mohammed Goni ya yi nuni da cewar, muddin dai ana so kasuwar ta zauna da gindinta ta yadda za ta rinka biyan bukatun kanta na yau da kullum har kuma ta yi tanadin wani abu don gobe, to kuwa ya zama wajibi ne ‘yan kasuwa su shiga kasuwar su tabbatar da cewar suna biyan kudaden hayan runfunar su a kan kari.

Da ya juya a kan tarihin kafuwar kasuwar, Gwamnan ya fadi cewa, a cikin watan Yuni na shekarar 1979 an wayi gari babbar kasuwar ta Maiduguri ta kama da wuta ta cinye kurmus sai toka kawai, wannan in ji Gwamnan, shi ya yi sanadiyar asarar dimbin dukiyar ‘yan kasuwar a wancan zamanin da rayukan wasu mutane.

Labarai Masu Nasaba

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

“Ko da yake gwamnatocin da suka gabata suna da shirin gina sabuwar kasuwa ta zamani a Maiduguri amma haka bai samu ba bisa ga dalilin da ban sani ba har yau, sai da muka hau Gwamnati.” In ji Gwamnan.

“Ba ko shakka wannan rana muhimmiya ce gare mu tun da mun zo gwamnati a yayin da wannan kasuwa ta zame toka kawai amma yau cikin ikon Allah ga shi muna bikin bude wannan damfareriya kuma ginannnar kasuwa wadda ba irin ta a duk fadin kasar nan.”

A kan yadda za a raba rufunan, Gwamnan ya ba da tabbatacin cewa za a yi rabon ne cikin adalci ba tare da la’akari da bambancin siyasa da addini ko kabila ba. Don haka sai ya roki ‘yan kasuwar da Allah bai ba su nasarar samun runfuna a cikin kasuwar ba da su yi hakuri su nema a wajen sababbin kantunan da ake ginawa a kan titin Sir. Kashim kusa da kantin Lebentis.

Alhaji Mohammed Goni ya fadi dai cewa, babu dai yadda za a ce kowa ya samu irin wadannan runfuna.
Da yake gabatar da nasa jawabin, Kwamishinan Raya Karkara na Jihar Alhaji Abba Zanna Mustapha ya fadi cewa, “Kasuwar ta kunshi runfuna iri dabam – dabam har 7,170.”

Kwamishinan ya ce wannan adadi na runfuna sun hada da dakunan ajiyar kayayyakin abinci (nama da kifi) har guda 310 da wurin sayar da abinci 60 da wurarren gyare – gyaren na’urori 10 da ofishin ‘yan sanda da na ‘yan kwana – kwana da masallaci da dai sauraren muhimman wuraren da a kan samu cikin kasuwanni irin na zamani.

Daga bisani kwamishinan ya za ga ya da Gwamnan dukkan sassan kasuwar.
Da yake bude sabuwar tashar Telebijin ta jihar, Alhaji Mohammed Goni ya ce ya zama wajibi ne ga gwamnatinsa ta kafa gidan Telebijin din kashin kanta.

Domin a cewarsa, “Kafofin watsa labarai na Gwamnatin Tarraya da ke Jihar ba su watsa irin ayyukan a zo a gani da Gwamnatinsa take yi.”

Gwamnan ya yi nuni da cewar irin wannan halayen gidaje watsa labaran na Gwamnatin Tarayya suka sanya Jihohin Kano da Anambra da Pleteau da Ikko suka kafa gidajen Telebijin din kashin kansu.

Alhaji Mohammed Goni ya ba da tabbacin cewa Gwamnatinsa ba ta nuna wani bambanci ko son kai ba wajen bayar da dama ga sauran Jam’iyyun siyasa na Jihar wajen amfani da gidan Telebijin din.

Tun farko da yake gabatar da jawabinsa, kwamishinan al’ummar cikin gida na watsa labarai da al’adun gargajiya na Jihar, Alhaji Abba Tor ya fadi cewa, “Saboda ganin yadda aikin ginin gidan Telebijin din zai dauka lokaci dangane da fatarar da ake fama da ita a kasar nan, ya sanya aka kasa aikin cikin hawa – hawa.”

A cewarsa, shirin farko da aka fara aiki da shi an kashe #1.5 miliyan, yayin da ake iya ganin shirye – shiryen tashar daga nisan kilomita 50 daga wajen garin Maiduguri. Alhaji Abba Tor ya ba da tabbacin cewa ana nan ana shirin wata doka da za a mika wa majalisar Dokokin Jihar don a samu a hada gidan Rediyon jihar da na Telebijin din da su zama abu gudu, watau a rinka kiran su Gidan Rediyo da Telebijin na Jihar.

A wata kuma, wakilinmu ya fahimci cewar yayin da Gwamnan ke bikin bude kasuwar su kuma ‘yan kwangilar kasuwar watau ‘SOGHAI NIG. LTD’ suna ciki suna kokarin kare ayyukan da suka rage kamar debe wa da sauran datti wanda ba a rasa ba.

Har ila yau dai kuma ba a sa wata rana takamaimai ba da za a bayar da izini ga ‘yan kasuwa su dawo cikin sabuwar kasuwar.
Wakilinmu ya fahimci cewa, dalilai biyu ya sa Gwamnantin jihar ta hanzarta bikin bude kasuwar, duk da kuwa akwai sauran aiki. Na farko dai shi ne neman biyan bukata siyasa na a ce Gwamna Alhaji Mohammed Goni ya yi aiki. Na biyu kuwa shi ne Bankin First Bank ya ba Gwamnatin Jihar rancen kudn ginin kasuwar ya fara uzurawa Gwamnatn Jihar da ta fara biyan bashin.

Wannan shi ne rohoton da Marigayi Ado Saleh Kankiya ya hada na bude babbar kasuwar ta Litinin da aka yi a shekarar 1983 bayan an sake gina ta.

A cikin shekarar 2015 ma an samu irin wannan iftila’in na gobara a cikin wannan babbar kasuwar inda aka tafka mummunar asara mai yawa. Bayan shekaru takwas kuma sai ga shi kasuwar ta sake konewar fiye da wanda aka yi a shekarun 1979 da kuma 2015. Ko wacce hanya da mataki ya kamata gwamnati da hukumar kasuwar ya kamata su bi wajen magance iftila’in gobara a wannan babbar kasuwa?

Za ku iya tura sakon kar-ta-kwata (tedt) ta wannan lambar 08069195272 ko kuma ku kira 08098331260 domin ba da shawarwarinku tare da gudunmawarku.

Mohammed Bala Garba (Mohammed Bawayo) ke muku fatan alheri daga birnin Maiduguri.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wani Tsohon Akanta Zai Sha Daurin Shekara 21 Kan Wawushe Miliyan 26

Next Post

Ba Zan Bar Shugabancin Barcelona Ba, Cewar Laporta

Related

Kasuwar Maiduguri
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

2 hours ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

1 day ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

1 week ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

1 week ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

2 weeks ago
Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

2 months ago
Next Post
Ba Zan Bar Shugabancin Barcelona Ba, Cewar Laporta

Ba Zan Bar Shugabancin Barcelona Ba, Cewar Laporta

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Kasuwar Maiduguri

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.