ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Waiwaye: Konewar Babbar Kasuwar Maiduguri A Shekarar 1979 Da Sake Gina Ta Da Aka Yi A 1983

by Muhammad Bala Garbasu
3 years ago
Kasuwar Maiduguri

Masu iya magana suka ce waiwaye adon tafiya. Duba da iftila’in gobarar da ya sake samun babbar kasuwar Litinin (Monday market) ta birnin Maiduguri ya sa naga dacewar yin waiwaye izuwa shekaru 44 baya domin sake kawo wa masu karatu wani rohoto da Marigayi Ado Saleh Kankiya ya hada na bude babbar kasuwar Litinin din da aka yi a shekarar 1983 bayan ta kone a shekarar 1979 an sake gina ta.

Wannan rohoton an buga shi a jaridar ‘GASKIYA TA FI KWABO’ a ranar Alhamis 11 ga watan Augusta a shekarar 1983 (har yanzu ina da jaridar). Ga yadda rohoton ya kasance kamar haka:

A RANAR Alhamis, 4/8/83, Gwamnan Jihar Borno, Alhaji Mohammed Goni ya yi bikin bude sabuwar babbar kasuwar Maiduguri wadda aka gina a kan #13 miliyan da sabuwar tashar Telebijin ta Jihar.
Da yake jawabi wajen bude babbar kasuwar, Gwamnan ya yi gargadi ga ‘yan kasuwar da za a rabawa runfunan da su tabbatar da cewar suna biyan kudaden runfunan cikin lokaci.

ADVERTISEMENT

Alhaji Mohammed Goni ya yi nuni da cewar, muddin dai ana so kasuwar ta zauna da gindinta ta yadda za ta rinka biyan bukatun kanta na yau da kullum har kuma ta yi tanadin wani abu don gobe, to kuwa ya zama wajibi ne ‘yan kasuwa su shiga kasuwar su tabbatar da cewar suna biyan kudaden hayan runfunar su a kan kari.

Da ya juya a kan tarihin kafuwar kasuwar, Gwamnan ya fadi cewa, a cikin watan Yuni na shekarar 1979 an wayi gari babbar kasuwar ta Maiduguri ta kama da wuta ta cinye kurmus sai toka kawai, wannan in ji Gwamnan, shi ya yi sanadiyar asarar dimbin dukiyar ‘yan kasuwar a wancan zamanin da rayukan wasu mutane.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

“Ko da yake gwamnatocin da suka gabata suna da shirin gina sabuwar kasuwa ta zamani a Maiduguri amma haka bai samu ba bisa ga dalilin da ban sani ba har yau, sai da muka hau Gwamnati.” In ji Gwamnan.

“Ba ko shakka wannan rana muhimmiya ce gare mu tun da mun zo gwamnati a yayin da wannan kasuwa ta zame toka kawai amma yau cikin ikon Allah ga shi muna bikin bude wannan damfareriya kuma ginannnar kasuwa wadda ba irin ta a duk fadin kasar nan.”

A kan yadda za a raba rufunan, Gwamnan ya ba da tabbatacin cewa za a yi rabon ne cikin adalci ba tare da la’akari da bambancin siyasa da addini ko kabila ba. Don haka sai ya roki ‘yan kasuwar da Allah bai ba su nasarar samun runfuna a cikin kasuwar ba da su yi hakuri su nema a wajen sababbin kantunan da ake ginawa a kan titin Sir. Kashim kusa da kantin Lebentis.

Alhaji Mohammed Goni ya fadi dai cewa, babu dai yadda za a ce kowa ya samu irin wadannan runfuna.
Da yake gabatar da nasa jawabin, Kwamishinan Raya Karkara na Jihar Alhaji Abba Zanna Mustapha ya fadi cewa, “Kasuwar ta kunshi runfuna iri dabam – dabam har 7,170.”

Kwamishinan ya ce wannan adadi na runfuna sun hada da dakunan ajiyar kayayyakin abinci (nama da kifi) har guda 310 da wurin sayar da abinci 60 da wurarren gyare – gyaren na’urori 10 da ofishin ‘yan sanda da na ‘yan kwana – kwana da masallaci da dai sauraren muhimman wuraren da a kan samu cikin kasuwanni irin na zamani.

Daga bisani kwamishinan ya za ga ya da Gwamnan dukkan sassan kasuwar.
Da yake bude sabuwar tashar Telebijin ta jihar, Alhaji Mohammed Goni ya ce ya zama wajibi ne ga gwamnatinsa ta kafa gidan Telebijin din kashin kanta.

Domin a cewarsa, “Kafofin watsa labarai na Gwamnatin Tarraya da ke Jihar ba su watsa irin ayyukan a zo a gani da Gwamnatinsa take yi.”

Gwamnan ya yi nuni da cewar irin wannan halayen gidaje watsa labaran na Gwamnatin Tarayya suka sanya Jihohin Kano da Anambra da Pleteau da Ikko suka kafa gidajen Telebijin din kashin kansu.

Alhaji Mohammed Goni ya ba da tabbacin cewa Gwamnatinsa ba ta nuna wani bambanci ko son kai ba wajen bayar da dama ga sauran Jam’iyyun siyasa na Jihar wajen amfani da gidan Telebijin din.

Tun farko da yake gabatar da jawabinsa, kwamishinan al’ummar cikin gida na watsa labarai da al’adun gargajiya na Jihar, Alhaji Abba Tor ya fadi cewa, “Saboda ganin yadda aikin ginin gidan Telebijin din zai dauka lokaci dangane da fatarar da ake fama da ita a kasar nan, ya sanya aka kasa aikin cikin hawa – hawa.”

A cewarsa, shirin farko da aka fara aiki da shi an kashe #1.5 miliyan, yayin da ake iya ganin shirye – shiryen tashar daga nisan kilomita 50 daga wajen garin Maiduguri. Alhaji Abba Tor ya ba da tabbacin cewa ana nan ana shirin wata doka da za a mika wa majalisar Dokokin Jihar don a samu a hada gidan Rediyon jihar da na Telebijin din da su zama abu gudu, watau a rinka kiran su Gidan Rediyo da Telebijin na Jihar.

A wata kuma, wakilinmu ya fahimci cewar yayin da Gwamnan ke bikin bude kasuwar su kuma ‘yan kwangilar kasuwar watau ‘SOGHAI NIG. LTD’ suna ciki suna kokarin kare ayyukan da suka rage kamar debe wa da sauran datti wanda ba a rasa ba.

Har ila yau dai kuma ba a sa wata rana takamaimai ba da za a bayar da izini ga ‘yan kasuwa su dawo cikin sabuwar kasuwar.
Wakilinmu ya fahimci cewa, dalilai biyu ya sa Gwamnantin jihar ta hanzarta bikin bude kasuwar, duk da kuwa akwai sauran aiki. Na farko dai shi ne neman biyan bukata siyasa na a ce Gwamna Alhaji Mohammed Goni ya yi aiki. Na biyu kuwa shi ne Bankin First Bank ya ba Gwamnatin Jihar rancen kudn ginin kasuwar ya fara uzurawa Gwamnatn Jihar da ta fara biyan bashin.

Wannan shi ne rohoton da Marigayi Ado Saleh Kankiya ya hada na bude babbar kasuwar ta Litinin da aka yi a shekarar 1983 bayan an sake gina ta.

A cikin shekarar 2015 ma an samu irin wannan iftila’in na gobara a cikin wannan babbar kasuwar inda aka tafka mummunar asara mai yawa. Bayan shekaru takwas kuma sai ga shi kasuwar ta sake konewar fiye da wanda aka yi a shekarun 1979 da kuma 2015. Ko wacce hanya da mataki ya kamata gwamnati da hukumar kasuwar ya kamata su bi wajen magance iftila’in gobara a wannan babbar kasuwa?

Za ku iya tura sakon kar-ta-kwata (tedt) ta wannan lambar 08069195272 ko kuma ku kira 08098331260 domin ba da shawarwarinku tare da gudunmawarku.

Mohammed Bala Garba (Mohammed Bawayo) ke muku fatan alheri daga birnin Maiduguri.

Kasuwar Maiduguri
Muhammad Bala Garbasu
+ postsBio
  • Muhammad Bala Garbasu
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bala-garbasu/
    Yajin Aikin ASUU: Mece Ce Makomar Daliban Jami’o’in Nijeriya? (Ra’ayi)

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Ba Zan Bar Shugabancin Barcelona Ba, Cewar Laporta

Ba Zan Bar Shugabancin Barcelona Ba, Cewar Laporta

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.