ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba A Son Raina Ummita Ta Rasu Ba –Dan China

by Sadiq
3 years ago
Dan China

Dan Chinan nan da ake zargi da yin kisan gilla ga budurwarsa Ummukulsum Sani Buhari da aka fi sani da Ummita, ya shaida wa kotu cewa bai so masoyiyar tasa ta mutu ba.

Mista Frank Geng Quarong shaida wa alkali haka ne a lokacin da aka sake gurfanar da shi a ranar Alhamis a kotun da ke zamanta a Kano.

  • An Yi Bikin Cika Shekaru 60 Da Sin Ta Fara Tura Tawagar Jami’an Lafiya Zuwa Ketare A Zimbabwe
  • Mutum 14 Sun Jikkata Yayin Da Magoya PDP Da APC Suka Yi Arangama A Bauchi

A zaman kotun na ranar ranar Alhamis, mai gabatar da kara kuma Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano, Batista M. A. Lawan ya tambaye Mista Quwangrong ko shi ya kashe Ummita?

ADVERTISEMENT

Shi kuma ya amsa da cewa, “Ni ban so ta mutu ba, kuma ba na so na mutu.”

Idan ba a manta ba, a shari’ar baya, Mista Geng Quangorong da ake zargi da zuwa gidan su Ummita ya yi mata kisan gilla,  yi ikirarin kashe mata kudi sama da Naira miliyan 100 cewa zata ta aure shi, amma daga baya ta juya masa baya, da ta ga ya tsiyace.

LABARAI MASU NASABA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

Da yake kare kansa a ranar Alhamis, ya gabatar wa kotun wani bidiyon da ya ce Ummita ce ta turo masa na gidan da take ginawa a Abuja.

Kotun ta sanya bidiyon da kuma wani bidiyon kayan bikin da dan Chinan ya yi ikrarin ya saya wa marigayiyar.

Amma mai gabatar da kara ya tambaye shi dalilin zuwansa gidan su marigayiyar ba tare da an gayyace shi ba, inda ya amsa da cewa dama can ya saba zuwa gidan.

Ya tambaye shi dalilin da bai yi wa mahaifiyar Ummita magana ba a lokacin da ta bude masa gidan, amma ya amsa cewa saboda ba sa fahimtar yaren juna ne.

Game dalilin shigarsa gidan kuwa, amsawa ya yi da cewa ya shiga ne don ya dauki karensa.

Har ila yau an tambayi Mista Geng ko shi ya kashe Ummita? Sai dai amsar wannan tambaya ta gagara, inda ya ce ‘Ni ban so ta mutu ba, kuma ba na so na mutu’.

Daga nan Alkalin Kotun Mai Shari’a Sanusi Ado Ma’aji ya dage shari’ar zuwa ranar 29 da 30 ga watan Maris, 2023 don ci gaba da sauraren shaidun kariya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Next Post
Gobara Ta Tashi A Kasuwar Katako Da Ke Bauchi 

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Katako Da Ke Bauchi 

LABARAI MASU NASABA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.