ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba A Son Raina Ummita Ta Rasu Ba –Dan China

by Sadiq
3 years ago
Dan China

Dan Chinan nan da ake zargi da yin kisan gilla ga budurwarsa Ummukulsum Sani Buhari da aka fi sani da Ummita, ya shaida wa kotu cewa bai so masoyiyar tasa ta mutu ba.

Mista Frank Geng Quarong shaida wa alkali haka ne a lokacin da aka sake gurfanar da shi a ranar Alhamis a kotun da ke zamanta a Kano.

  • An Yi Bikin Cika Shekaru 60 Da Sin Ta Fara Tura Tawagar Jami’an Lafiya Zuwa Ketare A Zimbabwe
  • Mutum 14 Sun Jikkata Yayin Da Magoya PDP Da APC Suka Yi Arangama A Bauchi

A zaman kotun na ranar ranar Alhamis, mai gabatar da kara kuma Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano, Batista M. A. Lawan ya tambaye Mista Quwangrong ko shi ya kashe Ummita?

ADVERTISEMENT

Shi kuma ya amsa da cewa, “Ni ban so ta mutu ba, kuma ba na so na mutu.”

Idan ba a manta ba, a shari’ar baya, Mista Geng Quangorong da ake zargi da zuwa gidan su Ummita ya yi mata kisan gilla,  yi ikirarin kashe mata kudi sama da Naira miliyan 100 cewa zata ta aure shi, amma daga baya ta juya masa baya, da ta ga ya tsiyace.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

Da yake kare kansa a ranar Alhamis, ya gabatar wa kotun wani bidiyon da ya ce Ummita ce ta turo masa na gidan da take ginawa a Abuja.

Kotun ta sanya bidiyon da kuma wani bidiyon kayan bikin da dan Chinan ya yi ikrarin ya saya wa marigayiyar.

Amma mai gabatar da kara ya tambaye shi dalilin zuwansa gidan su marigayiyar ba tare da an gayyace shi ba, inda ya amsa da cewa dama can ya saba zuwa gidan.

Ya tambaye shi dalilin da bai yi wa mahaifiyar Ummita magana ba a lokacin da ta bude masa gidan, amma ya amsa cewa saboda ba sa fahimtar yaren juna ne.

Game dalilin shigarsa gidan kuwa, amsawa ya yi da cewa ya shiga ne don ya dauki karensa.

Har ila yau an tambayi Mista Geng ko shi ya kashe Ummita? Sai dai amsar wannan tambaya ta gagara, inda ya ce ‘Ni ban so ta mutu ba, kuma ba na so na mutu’.

Daga nan Alkalin Kotun Mai Shari’a Sanusi Ado Ma’aji ya dage shari’ar zuwa ranar 29 da 30 ga watan Maris, 2023 don ci gaba da sauraren shaidun kariya.

MASU ALAKA

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi
Manyan Labarai

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

July 7, 2026
Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci
Manyan Labarai

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

July 7, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz
Manyan Labarai

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Next Post
Gobara Ta Tashi A Kasuwar Katako Da Ke Bauchi 

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Katako Da Ke Bauchi 

LABARAI MASU NASABA

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

July 7, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

July 7, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

July 7, 2026
Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026
Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

July 7, 2026
'yansanda

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

July 7, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.