• English
  • Business News
Monday, July 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsayin Da Dimukradiyyar Nijeriya Ta Kai A Yanzu – Buhari

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Matsayin Da Dimukradiyyar Nijeriya Ta Kai A Yanzu – Buhari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce yana shirin barin gidan gwamnati domin ya koma gidansa, yana aiki a gonakinsa da kiwon dabbobinsa sama da 300.

“Na kosa in bar gidan gwamnati,” in ji Buhari yake bayyana haka a fadar gwamnati da ke Abuja ranar Talata yayin da yake karbar jakadiyar Amurka, Mary Beth Leonard mai barin gado.

  • ‘Yan Nijeriya Sama Da Mutane 39 Ne Suka Mutu A Zaben 2023
  • Shema Ya Bai Wa PDP Sa’o’i 48 Ta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Masa

Ya ce idan aka yi la’akari da damar gudanar da zabe na gaskiya da kuma rashin tsoma baki kamar yadda aka gani a zabukan ranakun 25 ga Fabrairu da 18 ga Maris, ‘yan Nijeriya sun tabbatar da cewa sun iya tantance wanda zai jagorance su ba tare da wani ya gaya musu abin da za su yi ba.

Ya nuna jin dadinsa da gagarumin kishi ga dimokuradiyya da ‘yan Nijeriya ke nunawa ta zabin da suka yi a zaben 2023.

A cewar shugaban, wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Garba Shehu, ya fitar, ya ce da gaske dimokuradiyyar Nijeriya ta girma.

Ya ce: “Mutane sun fahimci ‘yancin da suke da shi. Idan aka ba da damar yin zabe na gaskiya da gaskiya, babu wanda zai iya gaya musu abin da zai yi. Ban ji dadin yadda wasu ‘yan takara suka fadi zabe ba.

“Amma na ji dadin yadda masu jefa kuri’a suka iya yanke zabar ra’ayinsu na wanda zai yi nasara da kuma wanda zai fadi. Duk da canjin kudin na rage zirga-zirgar kudade a hannun jama’a, amma sai da wasu suka raba kudin, na ce wa masu kada kuri’a su karbi kudin su yi zabi ra’ayinsu”

Ya ce ya gamsu da irin rawar da ya taka wajen gudanar da zaben ya tsaya a kansa, ba tare da tsoma baki ko wani tsangwama ba.Ya yaba wa jakadan mai barin gado cewa bisa ga dimbin nasarorin da aka samu a dangantakar Nijeriya da Amurka cikin shekara uku da rabi. Ya bayyana fatan Nijeriya za ta ci gaba da samun ci gaba wajen gina kasa daga cikin al’ummominmu daban-daban da masu fafutuka.

Tun da farko, Leonard ta bukaci a cire tallafin mai ya daga cikin muhimman shawarwarin da Buhari zai iya dauka kafin ya bar mulki a ranar 29 ga Mayu.

Ta ce ta yi farin ciki da irin ci gaban da aka samu a dangantakar Nijeriya da Amurka a cikin shekaru uku da rabi, musamman yadda aka kafa kwanan nan na tsarin bayar da biza na tsawon shekaru biyar tsakanin kasashen biyu, aiki tare a cikin tsaro da samar da kayan aikin soji da suka hada da jiragen yaki da jirage masu saukar ungulu na yaki masu zuwa nan ba da dadewa ba, da kuma hadin gwiwa a fannin kiwon lafiya don yaki da cutar kanjamau da kuma Korona tare da ba da tabbacin cewa Amurka za ta ci gaba da taimakawa wajen karfafa fannin kiwon lafiya a Nijeriya.

Ta bayyana godiyarta da na gwamnatin Amurka kan ci gaba da rawar da shugaban kasar ke takawa wajen tabbatar da tsaro a yankin Afirka da kuma karfafa tsarin dimokuradiyya a matsayin tsarin gwamnati, inda ta bayyana irin kakkausan martanin da ya bayar kan yawaitar juyin mulkin da aka yi a yammacin Afirka a baya-bayan nan a matsayin wanda bai dace ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

INEC Ta Yi Mun Daidai Da Ta Ayyana Zaɓen Gwamnan Adamawa Bai Kammalu Ba – Binani

Next Post

Muna Samun Tallafi Daga Sarkin Noman Masarautar Gaya – Kungiyar Manoman

Related

Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha

8 hours ago
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC
Manyan Labarai

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

1 day ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

1 day ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

2 days ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

2 days ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

2 days ago
Next Post
Muna Samun Tallafi Daga Sarkin Noman Masarautar Gaya – Kungiyar Manoman

Muna Samun Tallafi Daga Sarkin Noman Masarautar Gaya – Kungiyar Manoman

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

July 6, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

July 6, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

July 6, 2025
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

July 6, 2025
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

July 6, 2025
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

July 6, 2025
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

July 6, 2025
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

July 6, 2025
Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

July 6, 2025
Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.