ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Samun Tallafi Daga Sarkin Noman Masarautar Gaya – Kungiyar Manoman

by Mustapha Ibrahim
3 years ago
Gaya

Kungiyar manoma wadanda suka kunshi sarakunan noma na kananan hukumomin da ke cikin masarautar Gaya, sun bayyana cewa suna samun tallafi daga sarkin noman masarautar Gaya.

Sun bayyana hakan ne lokacin da suka ziyarci sarkin noman masarautar Gaya, Alhaji Yakubu Ibrahim Tagahu a ofishinsa a ranar Talata da ta gabata karkashin shugabancin sarkin noma na karamar hukumar Garko, Alhaji Shehu Umaru Garko.

  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Daina Muzgunawa Kamfanonin Waje
  • ‘Yan Nijeriya Sama Da Mutane 39 Ne Suka Mutu A Zaben 2023

Ya ce su manoman wannan masarauta da manoman wajen masarautar ta Gaya da ke Kano, suna samun tallafi mai dimbun yawa daga Alhaji Yakubu Ibrahim Tagahu.

ADVERTISEMENT

Alhaji Shehu ya ce sarkin noman masarautar Gaya shahararan manomi ne da ke noma hekta sama da dubu a shekara, kuma yakan samu daruruwan kayan amfanin gona a duk shekara.

Shi ma Alhaji Lawan Ta’anbo, jami’in tuntuba na hadadiyar kungiyar manoma na karamar hukumar Takai, wanda ya yi magana a madadin ayarin kungiyoyin manoman a ziyarar, ya ce sarkin noman masarautar Gaya na zuwa ko’ina a samu iri mai inganci ya gwada shi a kira manoma ya ba domin su amfana.

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Ya ce yana bai wa manona gudumawar injina, kudade da shawarwari da kuma bin hakkin manoma ko nemo musu tallafi a matakin gwamnatin jiha ko ta tarayya da sauran kungiyoyin bunkasa aikin noma na Nijeriya.

A karshe shi ma da yake jawabi wanda ya karbi ayyarin kungiyoyin manoman na masarautar Gaya, sarkin noman Gaya Alhaji Yakubu Ibrahim Tagahu, ya ce ba da tallafi ga al’uma umarni ne na addini kuma wajibi ne ga kowa ya yi haka mutukar yana da dama.

Ya kara da cewa umarnin da mai martaba sarkin masarautar Gaya, Dakta Ali Ibrahim Abdulkadir, ya jadada musu wannan umarni a lokacin nadasu kuma haka yake fada musu duk lokacin da ya kira su fada ko kuma suka ziyarceshi, saboda hakan ne zai kawo ci gaban masarautar Gaya da kuma Jihar Kano da ma Nijeriya gaba daya.

Gaya
Mustapha Ibrahim
+ postsBio
  • Mustapha Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/mustapha-ibrahim/
    Ma’aikatar REMASAB Ta Ƙaddamar Da Shirin Aikin Mai Da Shara Taki A Kano
  • Mustapha Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/mustapha-ibrahim/
    Cire Alamar PDP A Zaben Jihohi Biyu Ta Sa Sardauna Ya Nemo Wa Mabiyansa Mafita —Farfesa Sule Yau
  • Mustapha Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/mustapha-ibrahim/
    An Ƙirƙiro Da Shirin ‘Kano First’ Ne Don Sanya Wa Kanawa Kishin Jiharsu —Bala Gwagwarwa
  • Mustapha Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/mustapha-ibrahim/
    Idan Gwamna Abba Ya Ziyarci Kwalejin Bebeji Matsalarmu Za Ta Zo Ƙarshe – HOD Habib

MASU ALAKA

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Next Post
Falalar Ramadan Da Wasu Hukunce-hukuncen Azumi

Falalar Ramadan Da Wasu Hukunce-hukuncen Azumi

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.